• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Ilimi

Ilimin ‘ya mace: Fiye da ‘yan mata 40,000 a Kaduna sun amfana da shirin koyon dabarun rayuwa na Gwamna Uba Sani

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 16, 2026
in Ilimi
A A
0
Ilimin ‘ya mace: Fiye da ‘yan mata 40,000 a Kaduna sun amfana da shirin koyon dabarun rayuwa na Gwamna Uba Sani
Gwamna Uba Sani

Gwamna Uba Sani

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa fiye da ‘yan mata masu tasowa 40,000 a faɗin jihar sun amfana da wani tsari na musamman na koyon dabarun rayuwa, yayin da Gwamna Uba Sani ke shirin tabbatar da koyar da dabarun rayuwa a matsayin tsari na dindindin a dukkan makarantun sakandare na gwamnati.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta fitar, ta ce gwamnan na shirin gabatar da Ƙudirin Dokar Zartarwa ga Majalisar Dokokin jihar domin sanya koyon dabarun rayuwa a matsayin darasi tilas kuma na dindindin cikin manhajar makarantun sakandare na jihar.

Ana aiwatar da shirin koyon dabarun rayuwar ne ƙarƙashin Shirin AGILE (Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment) da Bankin Duniya ke tallafawa. Zuwa yanzu, shirin ya kai ‘yan mata 40,536 da maza 1,864, tare da horas da malamai 1,141 a matsayin masu jagoranci (mentors) a manyan makarantun sakandare a jihar.

Kwamishinan Ilimi, Farfesa Abubakar Sani Sambo, shi ne ya bayyana hakan a wani taron bitar dabaru da aka gudanar a Abuja kan yadda za a tabbatar da koyar da dabarun rayuwa a tsarin ilimi.

Da yake magana a madadin Gwamna Uba Sani, ya ce gwamnatin jihar ta ƙudiri aniyar wucewa ilimi na karatu kawai zuwa gina basirar tunani, juriyar zuciya, ƙwarewar jagoranci da alhakin zamantakewa, musamman ga ‘ya’ya mata.

Ya bayyana cewa wannan gyara alama ce ta sauyawa daga tsarin ilimi na gargajiya mai mayar da hankali kan “tunani” zuwa tsarin ilimi mai faɗi wanda ke ƙunshe da “aiki da ji”, domin shirya ɗalibai yadda ya kamata don fuskantar ƙalubalen rayuwa ta zahiri.

Manhajar dabarun rayuwar ta ƙunshi darussa kan ƙarfafa gwiwa, lafiya da abinci mai gina jiki, lafiyar haihuwa, hana tashin hankalin da ya shafi jinsi, sauyin yanayi da shigar kowa cikin al’umma.

Ma’aikatar ta ce sakamakon farko da aka samu ya haɗa da ƙaruwar ƙwarin gwiwar ɗalibai, raguwar yawan ƙin zuwa makaranta, ƙaruwar rajista, da sauye-sauyen ɗabi’a masu kyau, ciki har da ƙaruwar mutunta juna da tausayin juna a tsakanin ɗalibai.

Mai Kula da Shirin AGILE a Jihar Kaduna, Hajiya Maryam Sani Ɗangaji, ta tabbatar da cewa an aiwatar da shirin a dukkan manyan makarantun sakandare ba jihar.

Haka kuma, Daraktar Zartarwa ta Cibiyar Ilimin ‘Ya’ya Mata, Dakta Habiba Mohammed, ta bayyana tsarin Kaduna a matsayin abin koyi ga gyaran ilimi mai ɗorewa da ya mayar da hankali kan ‘ya mace.

Dangane da ƙudirin dokar da ake shirin gabatarwa, Shugaban Kwamitin Ilimi na Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Hon. Emmanuel Bako Kantiok, ya tabbatar da cewa a shirye majalisar take ta hanzarta amincewa da ƙudirin da zarar an kammala tattaunawa da masu ruwa da tsaki.

A cewar Ma’aikatar Yaɗa Labarai, dokar da ake shirin yi za ta kafa ingantaccen tsarin doka da kasafin kuɗi na musamman, domin tabbatar da cewa koyar da dabarun rayuwa—musamman ga ‘ya mace—zai ci gaba da kasancewa wani muhimmin ɓangare kuma tilas a tsarin ilimin gwamnati na Jihar Kaduna har zuwa shekaru da dama masu zuwa.

Tags: 'yanmataAGILEBankinDuniyadabarunrayuwaEmmanuelBakoKantiokFarfesaAbubakarSaniSamboGwamnaUbaSaniHabibaMohammediliminmataKadunaMa'aikatarIlimiMaryamSaniƊangaji
Previous Post

Kwankwaso ya ce a shirye yake ya shiga APC, amma ya gindaya sharuɗɗa 

Next Post

Tinubu yana kafa ginshiƙin cigaba mai ɗorewa tare da inganta rayuwar jama’a, inji Ministan Yaɗa Labarai

Related Posts

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya
Ilimi

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

April 26, 2026
NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795
Ilimi

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795

April 19, 2026
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi
Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

March 15, 2026
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ilimi

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

February 18, 2026
Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista
Ilimi

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

January 24, 2026
Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano
Ilimi

Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano

January 20, 2026
Next Post
Tinubu yana kafa ginshiƙin cigaba mai ɗorewa tare da inganta rayuwar jama’a, inji Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu yana kafa ginshiƙin cigaba mai ɗorewa tare da inganta rayuwar jama’a, inji Ministan Yaɗa Labarai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!