• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Siyasa

Tinubu yana gina ginshiƙi mai ƙarfi na makomar Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
November 27, 2025
in Siyasa
A A
0
Tinubu yana gina ginshiƙi mai ƙarfi na makomar Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris (a tsakiya), tare da shugabannin ƙungiyoyin goyon bayan jam’iyyar APC da suka kai masa ziyarar ban-girma a yau.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris (a tsakiya), tare da shugabannin ƙungiyoyin goyon bayan jam’iyyar APC da suka kai masa ziyarar ban-girma a yau.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu sun fara samar da ribar dimokiraɗiyya ga ‘yan ƙasa.

Ya faɗi haka ne a safiyar yau yayin tattaunawa da ƙungiyoyin goyon bayan jam’iyya mai mulki, wato APC, a ofishin sa da ke Radio House, Abuja.

Idris ya ce: “Mun cika da dama daga cikin alƙawurran kamfen ɗin mu. An kammala batun lamunin ɗalibai, mun kuma kawo ƙarshen almundahanar tallafin man fetur.

“Jihohin mu suna karɓar ƙarin kuɗi, ‘yancin ƙananan hukumomi ya zama na dindindin, kuma kowane yanki yanzu yana da hukumar cigaban sa.

“Tattalin arziƙin mu ya murmure, ajiyar kuɗin waje na ƙaruwa, hauhawar farashi tana raguwa.

“Mun fara manyan ayyukan raya ƙasa a dukkan sassa na tattalin arziki a shiyyoyin ƙasa guda shida.”

Kan batun sababbin umurnin Shugaba Tinubu game da tsaron ƙasa, Ministan ya jaddada cewa Shugaban Ƙasa ya amince da ɗaukar ƙarin jami’ai a sojoji da ‘yan sanda tare da tallafa wa sababbin rundunonin tsaro da gwamnatocin jihohi suka kafa, yana mai cewa wannan mataki zai zama babban sauyi a yaƙin da Nijeriya ke yi da rashin tsaro.

Ya ce: “Muna fuskantar gaggawar buƙatar kawar da ta’addanci da ‘yan bindiga, mu dawo da zaman lafiya, mu kuma ba ƙasar nan zaman lafiya ga kowa da kowa, ba tare da la’akari da ƙabila ko harshe ko addinin sa ba, kamar yadda kundin tsarin mulkin mu ya tanada.”

Ministan ya sake tabbatar da ƙudirin Gwamnatin Tarayya na yin duk mai yiwuwa don tabbatar da tsaron ƙasar nan.

A ɓangaren ƙarfafa matasa, Idris ya tabbatar da cewa Tinubu zai ci gaba da kare muradun matasa, ya ƙara da cewa a wannan gwamnati, matasa da ba a taɓa yi ba sun samu muƙamai na jagorantar ma’aikatu da hukumomi.

Idris ya shawarci ƙungiyoyin da su ci gaba da shiga cikin yaɗa shirye-shiryen gwamnati da faɗaɗa haskaka nasarorin ta da tasirin ta.

Ya jaddada cewa wajibi ne a tsaya tsayin daka cikin haɗin kai, tare da bin muradun asali da suka kafa suka APC kuma suka ɗore.

Shugabannin tawagar, Misis Adenike Abubakar da Dakta Abiola Moshood, a madadin ƙungiyoyin, sun sha alwashin ci gaba da bayar da goyon baya ga Ajandar Sabuwar Fata ta Shugaba Tinubu.

Tags: goyon bayaMohammed IdrisShugaba Bola Ahmed Tinubuƙungiyoyi
Previous Post

Tinubu ya yi matuƙar jimamin rasuwar babban malami, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi – Fadar Shugaban Ƙasa

Next Post

El-Rufai ya yanki katin shiga jam’iyyar ADC

Related Posts

An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano
Siyasa

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano

May 5, 2026
Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
El-Rufai ya yanki katin shiga jam’iyyar ADC

El-Rufai ya yanki katin shiga jam’iyyar ADC

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!