Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana matuƙar alhini kan rasuwar babban malamin addinin Musulunci, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a yau Alhamis yana da shekaru 101.
A cikin wata sanarwa da fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce rasuwar Sheikh Ɗahiru babban rashi ne ba kawai ga iyalai da mabiyan sa ba, har ma ga ƙasar nan gaba ɗaya, yana mai jaddada cewa marigayin ya sadaukar da rayuwar sa wajen shiryar da al’umma zuwa ga tafarkin gaskiya.
Shugaban ya bayyana Sheikh Ɗahiru Bauchi a matsayin jagoran Ɗariƙar Tijjaniyya da ya yi fice wajen wa’azi, karantarwa da kuma yaɗa zaman lafiya a tsakanin al’umma.
Ya ce: “Sheikh Ɗahiru Bauchi malami ne, uba, kuma muryar da ke kira da hikima da natsuwa. A matsayin fitaccen mai tafsirin Alƙur’ani, ya kasance ginshiƙi wajen ƙarfafa zaman lafiya da tsoron Allah. Mutuwar sa ta bar giɓi mai faɗi a wannan fage.”
Shugaban ya kuma tuna da addu’o’i da goyon bayan da Sheikh Ɗahiru ya ba shi a lokacin yaƙin neman zaɓen 2023.
Shugaban ya miƙa ta’aziyyar sa ga iyalan marigayin, mabiyan sa da dukkan al’ummar Musulmi a cikin ƙasar nan da waje.
Ya roƙe su da su ci gaba da ɗaukaka sunan marigayin ta hanyar bin koyarwar sa ta zaman lafiya, kyautata zamantakewa da ƙarfafa kusanci da Allah.







