Shugaba Bola Tinubu ya sabunta nadin Birgediya-Janar Mohammed Buba Marwa (ritaya) a matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) na tsawon wa’adin shekaru biyar.
Labarin yana ƙunshe cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a yau Juma’a.
Shi dai Marwa, gwamnatin Buhari ce ta fara naɗa shi muƙamin a cikin 2021 bayan ya yi aiki a matsayin Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Kawar da Shan Miyagun Ƙwayoyi tsakanin 2018 da 2020.
Sabon naɗin zai kai tabbatar da shi a matsayin shugaban hukumar har zuwa shekarar 2031.
Marwa, wanda ya kasance tsohon gwamnan jihohin Legas da Borno, ya samu horon soja a Nigerian Military School (NMS) da Nigerian Defence Academy (NDA).
Ya riƙe muƙamai da dama cikin rundunar sojin Nijeriya, ciki har da Brigade Major na 23 Armoured Brigade da Aide-de-Camp (ADC) ga tsohon Babban Hafsan Soji, Lt.-Gen. Theophilus Danjuma.
Ya kuma yi aiki a matsayin mataimakin mai bada shawara kan Tsaro a Jakadancin Nijeriya da ke Washington DC, da mai bada shawara kan tsaro ga Wakilan Nijeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya.
Marwa yana da digiri na biyu a fannin Public and International Affairs daga Jami’ar Pittsburgh (1983–85) da Master of Public Administration daga Jami’ar Harvard (1985–86).
A wa’adin sa na farko, NDLEA ta samu manyan nasarori, ciki har da kama masu safarar miyagun ƙwayoyi sama da 73,000 da kuma ƙwace ƙwayoyi masu nauyin fiye da kilo miliyan 15.
Haka kuma hukumar ta gudanar da manyan shirye-shirye kan wayar da kan jama’a game da illolin shan ƙwayoyi a faɗin ƙasar nan.
Tinubu, a saƙon sa, ya bayyana sake naɗin a matsayin tabbacin gamsuwa da jajircewar Marwa wajen yaƙi da fataucin da amfani da miyagun ƙwayoyi.
Ya ce: “Ina kira gare ka da ka ci gaba da jajircewa wajen fatattakar masu safarar ƙwayoyi da ke barazana ga makomar al’ummar mu, musamman matasa.”







