Hukumar kula da harkokin man fetur (Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority, NMDPRA) ta bayyana cewa ba za a aiwatar da ƙudirin ƙarin harajin kashi 15 cikin ɗari kan shigo da man fetur (PMS) da dizal ba.
Wannan bayanin yana ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, George Ene-Ita, ya fitar a shafin su na X a yau Alhamis, inda ya ce aiwatar da harajin da aka tsara ba ya cikin tsarin gwamnati a halin yanzu.
Hukumar ta tabbatar da cewa akwai wadataccen isasshen man fetur, dizal da iskar gas (LPG) a ƙasar nan, wanda ake samu daga masana’antun cikin gida da kuma shigo da su daga waje domin biyan buƙatar al’umma, musamman a lokacin buƙata ta musamman.
NMDPRA ta buƙaci ‘yan kasuwa da masu motoci da su guji ɓoye mai, saye da fargaba ko kuma ƙara farashi ba bisa ƙa’ida ba, tana mai cewa za ta ci gaba da sa ido a kasuwa tare da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da cewa babu tangarɗa wajen rabon man.
“Hukumar na gode wa dukkan masu ruwa da tsaki a sashen man fetur bisa ƙoƙarin su na tabbatar da isar mai ba tare da katsewa ba, kuma muna tabbatar da aniyar mu ta kare tsaron makamashi a ƙasar nan,” inji ta.







