Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Hon. Magaji Da’u Aliyu a matsayin Darakta Janar (MD) na Sheda Science and Technology Complex (SHESTCO), Abuja, cibiyar da ke da alhakin bincike da bunƙasa fasaha tare da kula da cibiyar binciken nukiliya ta ƙasa.
Haka kuma, shugaban ƙasar ya naɗa Injiniya Adesayo Olusegun Michael a matsayin Darakta Janar kuma Shugaban Hukumar Nigerian Electricity Management Services Agency (NEMSA), wacce ke kula da tabbatar da inganci da tsaro a harkokin wutar lantarki a Najeriya.
Sauran mambobin kwamitin NEMSA da aka naɗa sun haɗa da Injiniya Aliyu Abdulazeez (Daraktan Zartarwa, Fasaha); Ikechi Clara Nwosu (Shugaba, Kudu-maso-Gabas); Zubair Abdur’rauf Idris (Mamba); Igba Elizabeth (Mamba, Arewa ta Tsakiya); Sani Alhaji Shehu (Mamba, Arewa maso Gabas); Adeyemi Adetunji (Mamba, Kudu-maso-Yamma); Injiniya Emmanuel Eneji Nkpe (Mamba, Kudu-maso-Kudu) da Injiniya Charles Ogbonna Asogwa (Kudu-maso-Gabas).
A wani ɓangare, Shugaba Tinubu ya kuma miƙa sunayen Amina Gamawa (wakiliyar Jihar Bauchi) da Abdullahi Muktar (wakilin Jihar Kaduna) a matsayin kwamishinoni na Hukumar Revenue Mobilisation Allocation and Fiscal Commission (RMAFC).
An tura sunayen waɗannan mutane biyu zuwa Majalisar Dattawa domin tantancewa da amincewa, kamar yadda Bayo Onanuga, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar 10 ga Fabrairu, 2026.







