Tsohon Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Nijeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce murabus ɗin da ya yi daga hukumar ya samo asali ne daga dalilai a na ƙashin kan sa, bayan yin addu’a da tuntuɓar ‘yan’uwan sa.
A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kan sa domin sanar da murabus ɗin a hukumance, ya bayyana cewa ya miƙa takardar murabus ɗin sa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Ya ce: “Ina so in bayyana ƙarara cewa na ɗauki wannan mataki ne gaba ɗaya saboda dalilai na ƙashin kai. Bayan yin addu’a da nazari mai zurfi tare da tuntuɓar iyali na, na yanke wannan shawara cikin lamiri mai tsafta da kuma girmamawa ga alhakin hidimar jama’a mai tsarki.
“Cikin zurfin tunani da godiya ga Allah SWT, ina sanar da murabus ɗi na daga muƙamin Shugaba kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Nijeriya, wanda zai fara aiki daga Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.
“Dangane da tanade-tanaden Dokar NAHCON Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Nijeriya ta shekarar 2006, na miƙa murabus ɗi na a rubuce ga Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu (GCFR).”
Ya gode wa Shugaba Tinubu bisa amincewa da karramawar da ya yi masa ta naɗa shi domin yi wa Nijeriya da al’ummar Musulmi hidima a wannan matsayi.
“Amincewar da ka nuna a gare ni wata gata ce da zan riƙa alfahari da ita har abada. Ina kuma miƙa godiya ta ga Mai Girma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, bisa jagoranci, ƙarfafawa da goyon bayan da ya ba ni a tsawon lokacin da na yi a wannan muƙami.
“Ga mambobin Hukumar, ina miƙa godiya ta ta gaske. Ga jami’an gudanarwa da ma’aikatan Hukumar, na gode da haɗin kai, jajircewa da kuma ruhin aiki tare da kuka nuna. Ƙwarewar ku, juriyar ku da tsayuwar ku kan hidima sun kasance abin koyi.
“Haka kuma ina miƙa godiya ta ga abokan hulɗar mu – Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, kamfanonin yawon buɗe ido, kamfanonin jiragen sama da masu samar da ayyuka, da kuma takwarorin mu a Masarautar Saudiyya – waɗanda haɗin gwiwar su ya inganta ayyukan Hajjin Nijeriya sosai.”
Ya ƙara jaddada cewa murabus ɗin nasa ya samo asali ne kawai daga dalilai na ƙashin kai, kuma ba ya nuna wata rashin jin daɗi da Hukumar ko gwamnati ko kuma muhimmin aikin da suke aiwatarwa tare.
Ya ce: “Yayin da nake sauka daga wannan muƙami, addu’o’i na na tare da ku baki ɗaya. Ina roƙon Allah (SWT) cikin rahamar sa marar iyaka Ya karɓi ɗan ƙoƙarin mu, Ya shiryar da Ya albarkaci Shugaban Ƙasa da sabon shugabancin NAHCON, kuma Ya ba dukkan alhazai masu zuwa Hajji abin karɓaɓɓe (Hajj Mabrur).”







