Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da bayar da tallafin N250,000 ga ƙananan ‘yan kasuwa da matsakaitan masana’antu (MSME) da suka nuna bajinta a yayin Faɗaɗɗen Taron Ƙanana da Matsakaicin Masana’antu na Ƙasa (Expanded National MSME Clinic) da aka gudanar a Katsina.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shi ne ya bada wannan sanarwar a lokacin ƙaddamar da taro karo na 9 na shirin, wanda aka shirya don tallafa wa ƙanana da matsakaitan sana’o’i da kuma farfaɗo da tattalin arzikin al’umma.
Shettima ya bayyana cewa an samar da shirin ne domin kawo hukumomin gwamnati kusa da masu sana’a da kuma ƙarfafa fasahar ƙirƙire-ƙirƙire, samar da ayyukan yi, da sauƙaƙa samun rajista ko tallafi daga cibiyoyi kamar CAC, NAFDAC, SMEDAN, da Bankin Masana’antu.
Ya ce tallafin da Shugaba Tinubu ya amince da shi ba rance ba ne, wani ɓangare ne na yunƙurin gwamnati na cire shingen da ke hana ’yan kasuwa ci gaba.
Ya ƙara da cewa gwamnati ta kafa asusun naira biliyan 75 da sunan tallafin ga ƙananan masana’antu da ‘yan kasuwa (MSME Intervention Fund), wanda ke bai wa ’yan kasuwa rancen har zuwa naira miliyan 5 da kashi tara cikin ɗari a matsayin kuɗin ruwa, da kuma naira biliyan 50 a ƙarƙashin shirin Shugaban Ƙasa da ke bai wa ƙananan ’yan kasuwa tallafin kuɗi kyauta bisa wasu sharuɗɗa domin bunƙasa kasuwanci (Presidential Conditional Grant Scheme) da ke bada tallafin N50,000 ga ’yan kasuwa miliyan ɗaya a faɗin ƙasar nan.
Haka kuma gwamnatin ta samar da Asusun Tallafin Masana’antu daga Gwamnati (Manufacturers Fund) na naira biliyan 75 don tallafa wa masana’antu wajen rage tsadar samar da kayayyaki da sufuri.
Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ce sama da ’yan kasuwa 39,000 a Jihar Katsina sun amfana da shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya, inda aka raba naira biliyan 2.5 a matsayin tallafi da rance mai rangwame. A ƙarƙashin shirin RAPID, Shettima ya ce ’yan kasuwa 23 daga yankunan karkara sun samu fiye da naira miliyan 112 don faɗaɗa kasuwancin su.
Ya kuma yaba wa Gwamna Dikko Raɗɗa bisa kafa KASEDA, yana mai cewa Katsina na zama cibiyar cigaban masana’antu, noma, da kasuwancin yanar gizo a Arewacin Nijeriya.







