• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Kiwon Lafiya

Tinubu ya ƙaddamar da shirin kula da lafiyar mata don rage mace-macen mata masu juna biyu

Wakilin Mu by Wakilin Mu
September 12, 2025
in Kiwon Lafiya
A A
0
Tinubu ya ƙaddamar da shirin kula da lafiyar mata don rage mace-macen mata masu juna biyu
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a wajen bikin ƙaddamarwar

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a wajen bikin ƙaddamarwar

Shugaba Bola Ahmed Tinubu a yau ya ƙaddamar da wani sabon shiri da ake kira RenewHER, wanda manufar sa ita ce inganta lafiyar mata, musamman masu juna biyu, da kuma rage mace-macen mata a Nijeriya.

An gudanar da taron ƙaddamarwar ne a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilci shugaban ƙasar.

A jawabin sa, Tinubu ya ce lafiyar mata ita ce ginshiƙin cigaban kowace al’umma, don haka shirin zai kasance ginshiƙin haɗa kai tsakanin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki wajen bunƙasa kiwon lafiya a ƙasar nan.

Shirin RenewHER zai samar da ofishi na musamman na shugaban ƙasar kan lafiyar mata, wanda zai yi aiki tare da ma’aikatun lafiya da harkokin mata, da kuma ƙungiyar matan gwamnoni domin tabbatar da cewa an shigar da lafiyar mata cikin manufofin gwamnati a kowane mataki, daga jiha har zuwa ƙananan hukumomi.

Teburin manyan baƙi a taron

Bugu da ƙari, an sanar da kafa dandalin yanar gizo na lafiyar mata mai amfani da fasahar AI, wanda zai taimaka wajen yaɗa bayanai kan lafiyar iyaye mata da ’yan mata, kariya daga cututtuka, da kuma shirye-shiryen kiwon lafiya da ake buƙata a sassa daban-daban na ƙasar nan.

A nata jawabin, matar gwamnan Jihar Kwara, wadda kuma ita ce shugabar ƙungiyar matan gwamnoni, Farfesa Olufolake AbdulRazaq, ta ce RenewHER alama ce ta jajircewar gwamnatin Tinubu wajen inganta rayuwar mata da ƙarfafa masu gwiwa.

Ita ma mai bai wa shugaban ƙasa shawara ta musamman kan lafiyar mata, Dakta Adanna Steinacker, ta ce shirin RenewHER ya samo asali ne daga hangen nesa na Shugaba Tinubu na ɗaukar lafiyar mata a matsayin muhimmin al’amari na ƙasa.

Wasu mahalartan taron

Haka kuma, wakiliyar Ƙungiyar Matan Majalisar Ɗinkin Duniya (UN Women) a Nijeriya, Beatrice Eyong, ta bayyana shirin a matsayin “wani sauyi” kuma karo na farko da gwamnatin Nijeriya ta ɗauki irin wannan mataki a matakin shugabanci mafi girma.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da matan gwamnoni da kuma jakadu.

Kashim Shettima yana gabatar da jawabi a taron
Hoton mahalartan taron
Previous Post

Gwamnatin Kano Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Hassana Da Hussaina, Tagwayen Da Aka Haifa Manne Da Juna

Next Post

Etsu Nupe ginshiƙin zaman lafiya da haɗin kai ne a Nijeriya — Idris

Related Posts

Tinubu ya naɗa Fatima Zuntu shugabar hukumar NBMA
Kiwon Lafiya

Tinubu ya naɗa Fatima Zuntu shugabar hukumar NBMA

April 20, 2026
Likitoci za su fara yajin aiki na gama-gari daga Talata
Kiwon Lafiya

Likitoci za su fara yajin aiki na gama-gari daga Talata

April 5, 2026
Uwargidan Shugaban Ƙasa ta ƙaddamar da Asusun Ciyarwar Abinci na Ƙasa, ta ba da gudunmawar naira miliyan 500
Kiwon Lafiya

Uwargidan Shugaban Ƙasa ta ƙaddamar da Asusun Ciyarwar Abinci na Ƙasa, ta ba da gudunmawar naira miliyan 500

April 3, 2026
Ranar Ji ta Duniya 2026: Dalilan da za a iya kauce wa suna ci gaba da haddasa naƙasar ji a tsakanin yara a Nijeriya – Minista
Kiwon Lafiya

Ranar Ji ta Duniya 2026: Dalilan da za a iya kauce wa suna ci gaba da haddasa naƙasar ji a tsakanin yara a Nijeriya – Minista

March 3, 2026
Nijeriya ta rattaba hannu kan babbar yarjejeniyar zuba jari a fannin kiwon lafiya
Kiwon Lafiya

Nijeriya ta rattaba hannu kan babbar yarjejeniyar zuba jari a fannin kiwon lafiya

February 5, 2026
Amurka za ta kashe dala miliyan 200 na tallafi kai-tsaye ga fiye da asibitoci 900 na mabiya addinin Kirista a Nijeriya
Kiwon Lafiya

Amurka za ta kashe dala miliyan 200 na tallafi kai-tsaye ga fiye da asibitoci 900 na mabiya addinin Kirista a Nijeriya

December 21, 2025
Next Post
Etsu Nupe ginshiƙin zaman lafiya da haɗin kai ne a Nijeriya — Idris

Etsu Nupe ginshiƙin zaman lafiya da haɗin kai ne a Nijeriya — Idris

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!