• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Ilimi

Sarkin Kano Sanusi ya koma jami’a, ya yi rajista don karatun digirin Shari’a

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 15, 2026
in Ilimi
A A
0
Sarkin Kano Sanusi ya koma jami’a, ya yi rajista don karatun digirin Shari’a
Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Dakta Muhammadu Sanusi II

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Dakta Muhammadu Sanusi II

Sarkin Kano, Khalifa Dakta Muhammadu Sanusi II, ya koma ajin karatu bayan da aka ba shi izinin shiga karatun digirin farko (LL.B) a fannin Shari’ar Bature da Shari’ar Musulunci a Jami’ar Northwest da ke Kano.

An amince da wannan shigar karatu a hukumance ne ta cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 12 ga Janairu, 2026, wadda Shugaban Sashen Jarabawa, Shiga Makaranta da Tara Bayanai, Jafaru Muhammad, ya sanya wa hannu a madadin Magatakardan jami’ar.

An tabbatar da shigar karatun ne a yau Alhamis bayan tsohon mataimakin shugaban kasa, Bashir Ahmad, ya wallafa wasiƙar shigar karatun a kafar sada zumunta ta X (tsohon Twitter).

A cewar wasiƙar, an amince da shigar Sarkin ne bayan da ya miƙa buƙata ta musamman ga jami’ar, kuma aka amince da ita bayan ya cika sharuɗɗan da jami’ar ta gindaya don irin wannan la’akari ta musamman.

Wannan amincewa ta sanya mai martaba Sarkin Kano a matakin Level 200 a Kwalejin Shari’a, tare da fara aiki daga zangon karatu na shekarar 2024/2025.

Jami’ar ta ce masa: “Dangane da buƙatar ka ta neman shigar karatu ta musamman a wannan jami’a, na rubuto maka ne domin sanar da kai cewa jami’a ta amince da shigar karatun ka a Jami’ar Northwest, Kano, bayan ka cika sharuɗɗan da ake bukata don la’akari ta musamman.

“Saboda haka, an karɓe ka domin yin karatun digirin LL.B Common Law da Shari’a a Kwalejin Shari’a, Level 200, tare da fara aiki daga zangon karatu na 2024/2025.”

Jami’ar ta bayyana cewa shigar karatun yana bisa sharaɗin bin dukkan dokoki da ƙa’idojin da aka tanada a kundin jagoran ɗaliban Jami’ar Northwest.

Haka kuma, ta umurci Dakta Sanusi da ya kammala dukkan matakan rajista ta hanyar kai rahoto zuwa sassa daban-daban na jami’ar, ciki har da Daraktan Jarabawa, Shiga Makaranta da Tattara Bayanai, Sashen ICT, Sashen Kuɗi (Bursary), Ofisoshin Kwaleji da Sashen Karatu, Ɗakin Karatu na Jami’a, da kuma Sashen Harkokin Ɗalibai.

Dakta Sanusi, wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya ne, kuma fitaccen masanin tattalin arziki da ilimin Musulunci, ya shahara wajen neman ilimi da kuma fafutikar gyaran shugabanci, ilimi, da adalci a zamantakewa.

Matakin da ya ɗauka na neman digirin shari’a mai haɗe da Common Law da Shari’ar Musulunci ya ja hankalin jama’a, inda mutane da dama ke kallon sa a matsayin wani abin koyi a tsawon rayuwa, musamman a matakin shugabancin gargajiya mafi girma.

Previous Post

Za mu ba hukumar ƙidaya goyon baya, inji Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

Kwankwaso ya ce a shirye yake ya shiga APC, amma ya gindaya sharuɗɗa 

Related Posts

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya
Ilimi

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

April 26, 2026
NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795
Ilimi

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795

April 19, 2026
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi
Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

March 15, 2026
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ilimi

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

February 18, 2026
Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista
Ilimi

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

January 24, 2026
Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano
Ilimi

Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano

January 20, 2026
Next Post
Kwankwaso ya ce a shirye yake ya shiga APC, amma ya gindaya sharuɗɗa 

Kwankwaso ya ce a shirye yake ya shiga APC, amma ya gindaya sharuɗɗa 

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!