Sarkin Kano, Khalifa Dakta Muhammadu Sanusi II, ya koma ajin karatu bayan da aka ba shi izinin shiga karatun digirin farko (LL.B) a fannin Shari’ar Bature da Shari’ar Musulunci a Jami’ar Northwest da ke Kano.
An amince da wannan shigar karatu a hukumance ne ta cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 12 ga Janairu, 2026, wadda Shugaban Sashen Jarabawa, Shiga Makaranta da Tara Bayanai, Jafaru Muhammad, ya sanya wa hannu a madadin Magatakardan jami’ar.
An tabbatar da shigar karatun ne a yau Alhamis bayan tsohon mataimakin shugaban kasa, Bashir Ahmad, ya wallafa wasiƙar shigar karatun a kafar sada zumunta ta X (tsohon Twitter).
A cewar wasiƙar, an amince da shigar Sarkin ne bayan da ya miƙa buƙata ta musamman ga jami’ar, kuma aka amince da ita bayan ya cika sharuɗɗan da jami’ar ta gindaya don irin wannan la’akari ta musamman.
Wannan amincewa ta sanya mai martaba Sarkin Kano a matakin Level 200 a Kwalejin Shari’a, tare da fara aiki daga zangon karatu na shekarar 2024/2025.
Jami’ar ta ce masa: “Dangane da buƙatar ka ta neman shigar karatu ta musamman a wannan jami’a, na rubuto maka ne domin sanar da kai cewa jami’a ta amince da shigar karatun ka a Jami’ar Northwest, Kano, bayan ka cika sharuɗɗan da ake bukata don la’akari ta musamman.
“Saboda haka, an karɓe ka domin yin karatun digirin LL.B Common Law da Shari’a a Kwalejin Shari’a, Level 200, tare da fara aiki daga zangon karatu na 2024/2025.”
Jami’ar ta bayyana cewa shigar karatun yana bisa sharaɗin bin dukkan dokoki da ƙa’idojin da aka tanada a kundin jagoran ɗaliban Jami’ar Northwest.
Haka kuma, ta umurci Dakta Sanusi da ya kammala dukkan matakan rajista ta hanyar kai rahoto zuwa sassa daban-daban na jami’ar, ciki har da Daraktan Jarabawa, Shiga Makaranta da Tattara Bayanai, Sashen ICT, Sashen Kuɗi (Bursary), Ofisoshin Kwaleji da Sashen Karatu, Ɗakin Karatu na Jami’a, da kuma Sashen Harkokin Ɗalibai.
Dakta Sanusi, wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya ne, kuma fitaccen masanin tattalin arziki da ilimin Musulunci, ya shahara wajen neman ilimi da kuma fafutikar gyaran shugabanci, ilimi, da adalci a zamantakewa.
Matakin da ya ɗauka na neman digirin shari’a mai haɗe da Common Law da Shari’ar Musulunci ya ja hankalin jama’a, inda mutane da dama ke kallon sa a matsayin wani abin koyi a tsawon rayuwa, musamman a matakin shugabancin gargajiya mafi girma.







