Jagoran jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa bai ƙi shiga jam’iyyar APC ba, sai dai yana taka-tsantsan ne sakamakon abubuwan da suka faru a baya.
Kwankwaso ya faɗi hakan ne yayin da yake jawabi ga shugabannin jam’iyya da magoya bayan sa daga Rano da Dawakin Tofa a gidan sa da ke Kano a ranar Laraba, inda ya ce an yi kuskuren fahimtar matsayin sa.
Ya ce: “Ban ce ba zan shiga APC ba, amma dole ne a fara ba mu cikakken tabbaci game da makomar gwamnatin Jihar Kano kafin mu shiga APC.
“Mecece makomar ‘yan majalisun mu da sauran magoya bayan mu kafin mu amince mu sauya sheƙa?”
Tsohon gwamnan ya tuna da wasu haɗin gwiwar siyasa da aka yi a baya inda ɓangaren sa ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa gwamnatoci, amma daga bisani aka ci yaƙi aka bar su da kuturun doki.
Kwankwaso ya jaddada cewa duk wani sauya sheƙa da za a yi dole ne ya kasance bisa ga tabbatattun alƙawurra masu bayyana kariyar magoya bayan sa da tsarin gwamnatin Jihar Kano.
Ya kuma nanata cewa babu wata cikakken garanti da aka bayar har yanzu don kare muradun Kwankwasiyya ko tabbatar da adalci ga membobin ta a duk wata sabuwar haɗaka.
“Ba tare da rubutattun tabbaci ba, barin NNPP zai kasance gaggawa kuma abu mai haɗari,” inji shi.
Kwankwaso ya sake jaddada ƙudirin sa na kare amana da muradun magoya bayan sa, yana mai tabbatar masu da cewa ba za a ɗauki kowace irin shawara ba tare da tattaunawa mai faɗi da kuma tabbacin amfanin al’umma ba.







