• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Kwamandan soji ya umurci dakaru da “bin diddigin masu garkuwa ba tare da gajiyawa ba” domin ceto ɗaliban Neja da aka sace

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
November 23, 2025
in Labarai
A A
0
Kwamandan soji ya umurci dakaru da “bin diddigin masu garkuwa ba tare da gajiyawa ba” domin ceto ɗaliban Neja da aka sace
Kwamandan rundunar JTF ta "Operation Fansan Yamma" na yankin Arewa-maso-yamma, Manjo Janar Warrah Idris, yayin ziyarar sa a St. Mary’s Catholic School, Papiri, Ƙaramar Hukumar Agwara, Jihar Neja, a ranar Asabar

Kwamandan rundunar JTF ta "Operation Fansan Yamma" na yankin Arewa-maso-yamma, Manjo Janar Warrah Idris, yayin ziyarar sa a St. Mary’s Catholic School, Papiri, Ƙaramar Hukumar Agwara, Jihar Neja, a ranar Asabar

Kwamandan rundunar JTF ta “Operation Fansan Yamma” na yankin Arewa maso Yamma, Manjo Janar Warrah Idris, ya umurci dakaru da su ci gaba da matsa lamba kan miyagun da suka yi garkuwa da ɗaliban Makarantar Katolika ta Saint Mary’s (St. Mary’s Catholic School) da ke Papiri, Ƙaramar Hukumar Agwara, Jihar Neja, ba tare da sassauci ba.

Jami’in Yaɗa Labarai na “Operation Fansan Yamma”, Kyaftin David Adewusi, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa inda ya ce Idris ya yi wannan jawabi ne lokacin da ya ziyarci makarantar a jiya Asabar.

A yayin ziyarar, Kwamandan ya gudanar da binciken gaggawa a wurin da abin ya faru domin samun sahihin bayanin aiki kai-tsaye.

An tarbe shi tare da yi masa cikakken bayani daga Babban Hafsan Runduna ta 2 da kuma Kwamandan “Sector 3 OPFY’, Manjo Janar C.R. Nnebiefe, kan ƙoƙarin haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro domin ganin an kuɓutar da dukkan ɗaliban da aka sace.

Wani ma’aikacin makarantar yana yin bayani ga Kwamandan Sojan yayin ziyarar St. Mary’s Catholic School a ranar Asabar

Yayin da yake jaddada ƙudirin rundunar, Idris ya jaddada buƙatar ci gaba da bin diddigin miyagun, yana mai cewa, “’Yan bindigar suna jin zafin ayyukan mu kuma ba za su sami mafaka a ko’ina ba. Ku kasance masu sa ido kuma ku ci gaba da bin su ba tare da ba su hutu ba, har sai an kuɓutar da kowane ɗalibi gaba ɗaya kuma an mayar da su zuwa ga iyalan su.”

Yayin da yake bayyana ƙwarin gwiwar sa a kan dakarun, ya tabbatar da cewa za a samar da dukkan kayan aiki da tallafi da duk wata buƙata ta aiki domin tabbatar da nasarar wannan aiki.

Tags: Manjo Janar Warrah IdrisOperation Fansan YammaPapirisace ɗalibaiSt. Mary’s Catholic School
Previous Post

Matsalar tsaron Nijeriya tana hana ni barci, inji Tinubu a taron cikar ACF shekaru 25

Next Post

Albashin Ronaldo da na Sadio Mane a 2025 ya nuna yadda ‘yan ƙwallo ke samun kuɗi fiye da ‘yan kasuwa 

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Albashin Ronaldo da na Sadio Mane a 2025 ya nuna yadda ‘yan ƙwallo ke samun kuɗi fiye da ‘yan kasuwa 

Albashin Ronaldo da na Sadio Mane a 2025 ya nuna yadda 'yan ƙwallo ke samun kuɗi fiye da 'yan kasuwa 

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!