• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Ilimi

Gwamnatin Tarayya ta buɗe rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na PTDF

Wakilin Mu by Wakilin Mu
January 20, 2026
in Ilimi
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta buɗe rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na PTDF
Tambarin ba da guraben karatu na PTDF

Tambarin ba da guraben karatu na PTDF

Gwamnatin Tarayya ta bayyana buɗe fara rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na shekarar 2026 ƙarƙashin Hukumar Haɓaka Fasahar Man Fetur (Petroleum Technology Development Fund, PTDF) domin bai wa ɗaliban Nijeriya damar karatun digiri na biyu (MSc) da digiri na uku (PhD) a Birtaniya, Jamus, Faransa da Malaysia.

Sanarwar ta fito ne ta shafin X na Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Sadarwa ta Zamani, Dada Olusegun, a jiya Litinin.

Sanarwar ta ce an fara karɓar rajistar masu neman guraben karatun PTDF na ƙasashen waje na 2026.

A cewar bayanin da PTDF ta wallafa a shafin ta na intanet, shiri ne na masu neman MSc da PhD a fannoni da suka shafi harkar mai da iskar gas, inda tsarin zai ɗauki nauyin kuɗin karatu, tikitin jirgi na zuwa da dawowa, masauki, alawus na rayuwa, inshorar lafiya, da kuɗin bincike (bench fees).

PTDF ta bayyana cewa shirin zai bai wa waɗanda suka samu guraben horo da kayan bincike na zamani a matakin duniya, tare da ƙarfafa ƙwarewar ’yan Nijeriya a fannin mai da iskar gas.

Ga masu neman PhD a Birtaniya, an tanadi tsarin split-site, inda za a gudanar da bincike tsakanin College of Petroleum and Energy Studies, Kaduna (CPESK) da wasu jami’o’in haɗin gwiwa a Birtaniya, ciki har da Robert Gordon University, University of Strathclyde, da University of Portsmouth.

Hukumar ta jaddada cewa gurabe ne da ake tsananin gasa, inda za a tantance masu nema bisa ƙwarewar ilimi, shirin bincike, kasancewa cikin ƙungiyoyin ƙwararru, da kuma dacewar karatun da harkar mai da iskar gas.

Sharuɗɗan MSc sun haɗa da samun aƙalla Second Class Lower (2.2) ko 2.1 a digiri na farko, kammala NYSC, iya amfani da kwamfuta, da samun Credit a sakamakon O’Level biyar, ciki har da Turanci da Lissafi.

Masu neman PhD kuma dole su gabatar da shirin bincike na shafuka biyar wanda zai fayyace manufofi, dabarun aiwatarwa, da hanyoyin tattara bayanai.

PTDF ta ƙara da cewa za a tantance NIN na duk masu nema kafin cike fom, tare da gargaɗin cewa maimaita rajista ko gabatar da takardu na bogi zai haifar da cire mutum kai-tsaye.

An shawarci masu sha’awa su nemi guraben ta yanar gizo a scholarship.ptdf.gov.ng bisa tsare-tsaren da aka amince da su a jami’o’in abokan hulɗar PTDF.

Za a rufe rajistar a ranar 27 ga Fabrairu, 2026.

Tags: gurabekaratuPTDFscholarships
Previous Post

Abdul’aziz ya wakilci Shugaban Ƙasa a wajen ta’aziyyar mata da ‘ya’yan ta shida da aka kashe a Kano

Next Post

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kai domin ƙarfafa martabar Nijeriya a idon duniya

Related Posts

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya
Ilimi

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

April 26, 2026
NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795
Ilimi

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795

April 19, 2026
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi
Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

March 15, 2026
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ilimi

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

February 18, 2026
Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista
Ilimi

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

January 24, 2026
Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano
Ilimi

Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano

January 20, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kai domin ƙarfafa martabar Nijeriya a idon duniya

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kai domin ƙarfafa martabar Nijeriya a idon duniya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!