Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yaɗa Labarai, Malam Abdul’aziz Abdul’aziz, a yau ya wakilci Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu wajen ta’aziyyar iyalan Malam Haruna da aka yi wa matar sa da ‘ya’yan su guda shida kisan gilla a Kano.
A gidan, Abdul’aziz ya yi ta’aziyya ga maigidan tare da tabbatar masa da cewa Shugaban Ƙasa ya ba da umurni da a tabbatar da an yi gaggawar yanke wa waɗanda suka yi wannan aika-aikar hukunci kamar yadda dokar ƙasa ta tanadar.
Haka kuma ya je ta’aziyyar babban ɗan kasuwar nan Dakta Abdul’aziz Bature wanda Allah ya yi wa rasuwa kwana uku da suka wuce, inda ya yi wa iyalai da ‘yan’uwa da abokan arziki gaisuwa a madadin Shugaba Tinubu.

A ƙarshe ya yi addu’ar Allah ta’ala ya jiƙan su da rahama baki ɗaya, amin.







