Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da ɗaukar masu gadi mutum 1,600 aikin dindindin don kula da makarantun sakandare a faɗin jihar.
Kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa inda ya ce gwamnan ya ce wannan babban mataki ne da aka ɗauka don kawo kwanciyar hankali da ɗa’a a makarantun gwamnati.
Ya ce tabbatar da yanayin tsaro ga ɗalibai da malamai da kayan makaranta abu ne mai muhimmanci ga gwamnatin sa, tare da la’akari da cewa karatu ba zai yiwu ba a inda babu kwanciyar hankali.
Gwamna Yusuf ya ce masu gadin za su taka muhimmiyar rawa wajen tsare lafiyar makarantu tare da sa ido kan ayyukan da ba su dace ba, da kuma mara wa aikin gudanar da makarantun baya.
Ya yaba wa Ma’aikatar Ilimi ta jiha da hukumar KSSSSMB saboda sadaukarwar su wajen aiwatar da umurnin gwamnati.
Gwamnan ya yi kira ga sababbin masu gadin da su gudanar da aikin su cikin lura, ɗa’a da tsare mutunci.







