Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana cewa hanya mafi ma’ana ta girmama tarihin tsohon Shugaban Ƙasa Janar Murtala Ramat Muhammed ita ce ci gaba da aiki domin gina ƙasa da za ta rayu bisa aƙidun da ya ginu a kan su.
Sanwo-Olu ya faɗi haka ne a wajen taron tunawa da Janar Murtala shekaru 50 bayan rasuwar sa.
Shi dai Janar Murtala, an kashe shi ne a yunƙurin juyin mulkin da wasu sojoji ‘yan tawaye suka yi a ranar 13 ga Fabrairu, 1976.

A taron da aka yi yau a Legas, gwamnan ya ce: “Shekaru hamsin bayan rasuwar Janar Murtala Muhammed, misalin sa har yanzu yana da nauyi a zukatan mu wajen fahimtar nauyin da ke kan mu a matsayin ma’aikatan gwamnati.
“Ya jagoranci ƙasa da tsafta da tsayin daka. Ya buƙaci ladabi da bin ƙa’ida daga ma’aikatan gwamnati, kuma ya ɗauki muryar Nijeriya da ƙwarin gwiwa zuwa ƙasashen waje, musamman a batutuwan adalci da haɗin kan Afrika.

“Rayuwar sa tana ci gaba da zama tunatarwa cewa shugabanci ba wai tsawon lokacin zama a ofis ba ne, amma game da ƙudiri da jarumtakar ɗaukar mataki idan an kira mutum.
“A yau, a wannan gagarumin bikin cika shekaru, ina tunawa da ma’aunin da ya kafa. Dole ne gwamnati ta kasance mai ƙa’ida, mai mayar da hankali kan manufa, kuma haɗaɗɗiya wajen cimma buri guda.
“Hanya mafi ma’ana ta girmama tarihin sa ita ce ci gaba da aiki domin gina ƙasa da za ta rayu bisa waɗannan ƙimomi.”










