Maganar dai ɗaya ce tun daga kasuwar Pataskum har ta Bakori. Daga kasuwar Ɗandume har ta Shuwarin. Tun daga kasuwar hatsi ta Giwa har ta Sabuwa, Charanci, Badume, Maigatari da duk wata kasuwar da ake kai amfanin gona a sayar. Ba ka jin ana labarin darajar farashin amfanin gona, sai dai faɗuwar sa ragaraga.
Gero, dawa, wake, masara, gyaɗa, rogo, barkono, riɗi, albasa, shinkafa duk farashin su sai ƙara yin ƙasa yake yi a kullum.
Lamarin ya zama fuska biyu: A fuska ɗaya talakawan da ba noma suke yi ba, sai dai idan manoma sun noma su je su saya, murna suke ta yi da addu’a, Allah ya ƙara karya farashin kayan abinci. A ɗaya gefen kuma manoma sai kuka suke yi, saboda ganin cewa kashi 90 bisa 100 na manoman Arewa da suka yi noma a daminar bana, sun ɗibga gagarumar asara.
Wannan ce ta sa har a cikin makon da ya gabata, Majalisar Dattawa ta zartar da riƙon Shugaba Bola Tinubu ya dubi mummunan halin da manoma suka shiga, ya tallafa masu da ɗan abin da za su goge hawayen kukan da suke ci gaba da yi tun cikin damina, har yanzu bayan kaka ba su daina ba.
Wannan matsala da manoma suka afka, ta samo asali ne daga tsadar da amfanin gona ya yi a 2023 da kuma 2024. Ganin haka, sai Gwamnatin Tarayya ta cire waigin harajin kayan abincin da ake shigowa da shi daga waje. Hakan ya sa aka riƙa shigo da kayan abinci masu yawan da suka cika kasuwanni. Wannan ya tilasta saukar farashin kayan abinci sosai, har ta kai malejin tsadar rayuwa da malejin hauhawar farashi sun sauka ƙasa sosai, daidai aljihun talaka, a cikin 2025.
Manoman asali da manoman neman riba sun yi tunanin cewa kayan abinci zai sake tsada, kamar yadda ya yi a shekaru biyu da suka gabata. Sai kowa ya koma noma. Ko dai don ya noma wanda za a ci a gida, ya huta da saye, ko kuma domin ya sayar idan kayan gona sun yi tsada.
Sai dai abin bai zo wa manoma yadda suke so a 2025 ba. Domin tun a farkon damina suka fara ganin ba daidai ba. Sai da ta kai buhun takin zamani ya kai har kusan naira 60,000.
“To yanzu fa idan za ka sayi buhun takin zamani, sai ka kusan sayar da buhun masara uku. Har naira 21,000 ana sayar da buhun masara a cikin Disamba ɗin nan.” Inji Imamu Nuhu, wani manomin da bai ji daɗin daminar bana ba, saboda asarar da ya ce ya ɗibga.
Shi kuwa Junaidu Murnai ƙara nitso ya yi wajen yi wa wakilin mu bayanin wannan asara da manoma suka yi. Cewa ya yi, “kana ganin ana sayar da buhun masara naira 20,000 ko? To ina tabbatar maka, baya ga asarar kuɗin noma da na huɗa da na taki, duk buhun masara ɗaya kafin a kai shi kasuwa sai manomi ya yi masa wahalar naira 6,000 zuwa 7,000. Ka ga dai za a cire nasarar, ta tara wuri ɗaya, a cashe ta. A sayi buhuna a zuba. Duk ba kyauta leburori za su yi wa manomi ba.
“Daga nan za ka nemi mota ta ɗauko maka zuwa gida, ko a kai maka kasuwa. To a wannan ranar za ka san fetur ya yi tsada. Idan direba ya yanka maka kuɗin da za ka biya, sai ka ji kamar ka bar amfanin gonar a daji kawai, saboda baƙin ciki.”
Wata matsala da manoman ke fuskanta a yanzu ita ce, faɗuwar farashin kayan abinci ya sa ko sun kai kasuwa sun sayar, ba su iya biyan buƙatu na dole da na yau da kullum ɗin da suke son su biya. “Babu abin takaici kamar yadda wai sai ka sayar da tiya uku ta dawa za ka iya sayen tiyar garin kwaki ɗaya da kuɗin. Gaskiya da sakel.” Inji wani manomi a Garki, Jihar Jigawa.
A halin yanzu masu sayen abinci suna kimshewa sai ya yi tsada su sayar, su ma sun shiga taitayin su. Domin daminar bana an yi noma sosai, kuma a kullum sai fitar da shi a kasuwa ake yi. Babu wanda ya san yadda kasuwar hatsi za ta kasance nan da watanni bakwai da za a fuskanta. Tabbas idan ma ya nemi ya sake tsada, to gwamnati na iya karyar da shi, kamar yadda ta yi a 2025.
Saura abin da za a zura ido a gani, shin ko gwamnatin za ta dubi irin asarar da manoma suka yi har ta tallafa masu kamar yadda Majalisar Dattawa ta nemi ta yi?
Sai dai kuma da dama daga waɗanda suka maida noma kasuwanci, musamman masu karɓar hayar gonaki, ba za su sake gangancin yin noma a daminar 2026 ba. To akwai tsoron kada hakan ya haifar da ƙarancin abinci, nan da watanni goma masu zuwa.







