• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Bankin Duniya ya yaba da cigaban gyare-gyaren tattalin arziki da Nijeriya ke yi

Fatima Abdullahi by Fatima Abdullahi
February 5, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Bankin Duniya ya yaba da cigaban gyare-gyaren tattalin arziki da Nijeriya ke yi
Ministan Kuɗi da Daidaita Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, tare da Manajan Daraktar Ayyuka na Rukunin Bankin Duniya, Misis Anna Bjerde, da manyan jami'ai a ƙarshen taron

Ministan Kuɗi da Daidaita Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, tare da Manajan Daraktar Ayyuka na Rukunin Bankin Duniya, Misis Anna Bjerde, da manyan jami'ai a ƙarshen taron

Rukunin Bankin Duniya ya yi maraba da cigaban gyare-gyaren da Nijeriya take yi tare da yaba wa Gwamnatin Tarayya kan fayyace manufar ta, yana mai cewa ana samun ƙaruwar amincewa daga kasuwannin duniya da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa.

Hakan ya bayyana ne daga wani taro da aka gudanar a wannan makon a Abuja tsakanin Ministan Kuɗi da Daidaita Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, da Manajan Daraktar Ayyuka ta Rukunin Bankin Duniya, Misis Anna Bjerde, tare da manyan jami’ai.

Tattaunawar ta mayar da hankali kan faɗaɗa samar da ingantacciyar wutar lantarki, ƙarfafa harkar noma, hanzarta bunƙasa kayayyakin more rayuwa na dijital, inganta zirga-zirgar kasuwanci, da kuma buɗe ƙofofin zuba jari daga ɓangaren ‘yan kasuwa — waɗanda dukkan su muhimmai ne wajen gina tattalin arziki mai ƙarfi da gasa.

Misis Bjerde ta sake jaddada goyon bayan Bankin Duniya ga ajandar bunƙasa tattalin arzikin Nijeriya ta hanyar zuba jari, tare da mai da hankali kan aiwatar da ayyukan more rayuwa da kuma sa hannun ɓangaren ‘yan kasuwa.

Mista Wale Edun yana miƙa kyautar hoto a madubi ga Misis Anna Bjerde, a ƙarshen taron

A jawabin sa, Mista Edun ya bayyana cewa ana samun gagarumin cigaba a muhimman fannoni, sakamakon tsare-tsaren manufofi masu ƙarfi da kuma sabunta mayar da hankali kan bunƙasa tattalin arziki, jawo jari, da samar da ayyukan yi.

Ya kuma sake tabbatar da jagorancin Nijeriya a gyaran fannin makamashi da burin ta na zama cibiyar tattalin arziki ta yankin, tare da goyon bayan rawar da Nijeriya take takawa a matsayin ta na hedikwatar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika (ECOWAS).

Ɓangarorin biyu sun amince kan hanzarta aiwatar da shirye-shirye, jawo manyan jarin kuɗi, da samar da dama ga yawan al’ummar Nijeriya da ke ƙaruwa.

Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya, Malam Mohammed Manga, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa taron ya sake tabbatar da sahihiyar alƙiblar tattalin arziki ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma ƙaruwar amincewar duniya da shirin gyare-gyaren ƙasar nan yake samu.

“Wannan muhimmin mataki yana nuna jajircewar Nijeriya wajen samun bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa tare da sanya ƙasar a sahun gaba a kasuwannin yankuna da na duniya,” inji shi.

Tags: AnnaBjerdetaroTattalinArzikiWaleEdun
Previous Post

Nijeriya ta rattaba hannu kan babbar yarjejeniyar zuba jari a fannin kiwon lafiya

Next Post

Sauye-sauyen tattalin arzikin Tinubu suna daidaita Nijeriya — Idris

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Next Post
Sauye-sauyen tattalin arzikin Tinubu suna daidaita Nijeriya — Idris

Sauye-sauyen tattalin arzikin Tinubu suna daidaita Nijeriya — Idris

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!