Tsohon Ministan Tsaro, Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi gargaɗin cewa barin gwamnonin jihohi su kafa kuma su yi amfani da rundunonin ‘yan sa-kai “marasa isasshen horo na ƙwararru” zai ƙara yawaitar yaɗuwar ƙananan makamai da manyan makamai cikin sauƙi a faɗin ƙasar nan.
A cikin wata sanarwa ga manema labarai, Kwankwaso ya ce amincewar Gwamnatin Tarayya da wannan mataki, ko da kuwa an yi shi da kyakkyawar niyya ne, ya riga ya ƙarfafa wasu mutane su fara kafa nasu rundunar tsaro nasu na kan su, wanda hakan ke ƙara barazana ga zaman lafiyar da ake ciki.
Ya ce: “Abubuwan da ke faruwa kwanan nan a ƙasar mu sun cika ni da damuwa matuƙa game da halin da al’amuran ƙasar mu ke ciki.
“Ni da na yi aiki a cikin tsarin a tsawon shekaru, na san cewa babban nauyin yaƙi da rashin tsaro a Nijeriya ya rataya ne a wuyan Gwamnatin Tarayya tare da haɗin kai da gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.
“Abin takaici, kamar Gwamnatin Tarayya ta kasa shawo kan lamarin.
“Hakan ya bayyana a yadda ta amince da barin jihohi su kafa su kuma tura rundunonin ‘yan sa-kai ba tare da horon ƙwararru ba.
“Wannan mataki, ko da an yi shi da niyya mai kyau, yana haifar da yawaitar ƙananan makamai da manyan makamai ba tare da kulawa ba a faɗin ƙasar nan.
“Abin da ya fi muni ma, wasu mutane sun fara amfani da wannan damar wajen kafa nasu dakarun tsaron, kamar yadda ake gani daga wasu ‘yan siyasa. Wannan yana ƙara barazana ga zaman lafiyar ƙasar mu.”
Jagoran na rundunar siyasa ta Kwankwasiyya kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano ya ƙara da cewa: “Wani abin damuwar kuma shi ne yadda ake ƙara yawan nuna bambancin ƙabilanci da na yanki ga ‘yan Nijeriya a ƙasar su. A ‘yan kwanakin nan mun ga rahotanni masu tayar da hankali na yadda ake kama mutane – musamman daga wani yanki – ba bisa ƙa’ida ba, ana tsare su, ana cin zarafin su, a wasu lokuta ma ana azabtar da su a wasu sassan ƙasar nan.
“Hakan ya ƙara muni saboda yaɗa tsangwama, barazana da kalaman ƙiyayya a kafofin sada zumunta, wanda sau da yawa ake tunzura shi saboda son zuciya na ƙabilanci da addini. Waɗannan abubuwa barazana ce mai girma ga haɗin kan ƙasa.”
Ya kira Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin daƙile “waɗannan abubuwa masu haɗari kafin su ƙara fita daga hanya.”
Ya ce: “A matsayi na na tsohon Ministan Tsaro kuma Shugaban Kwamitin Kula da Yaɗuwar Ƙananan Makamai da Manyan Makamai, abin yana ba ni tsoro matuƙa ganin yadda ake yawo da makamai cikin sauƙi a ƙasar nan — wanda bai dace ba.”
Kwankwaso ya taya Janar Christopher Gwabin Musa (mai ritaya) murnar samun “naɗin da ya dace da shi ƙwarai” a matsayin Ministan Tsaro.
Ya ce: “Ina da yaƙinin cewa, idan akwai cikakken ƙwarin gwiwar siyasa da goyon baya, yana da ƙwarewar da da ake buƙata wajen taka rawar gani domin dawo da tsaro da kwanciyar hankali ga ƙasar mu.”







