• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba

ALI KANO by ALI KANO
May 8, 2026
in Labarai
A A
0
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Alhaji Abdullahi Bello Boɗejo

Alhaji Abdullahi Bello Boɗejo

Jami’an tsaro sun kama ɗan takarar neman kujerar Sanata mai wakiltar Taraba ta Tsakiya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, Alhaji Bello Boɗejo, a daren jiya Alhamis a Jalingo, babban birnin Jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Boɗejo, wanda shi ne shugaban ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah Kautal Hore, ya je Jalingo tun da farko a cikin jirgin sama mai zaman kan sa ta filin jirgin sama na Ɗanbaba Suntai da misalin ƙarfe 1:20 na rana.

Dubban magoya bayan sa daga ƙananan hukumomi biyar da suka haɗa yankin sanatocin Taraba ta Tsakiya sun tarbe shi.

Da yake magana da Daily Trust ta wayar tarho, mataimakin sa na musamman, Umar, ya ce an kama ɗan takarar APC ɗin ne bayan ya kai ziyara wasu ofisoshin hukumomin tsaro tare da wasu na kusa da shi a siyasa.

A cewar sa, an kama shi ne a ɗaya daga cikin ofisoshin tsaron jim kaɗan bayan ya yi jawabi ga magoya bayan sa a sakatariyar APC ta jihar da ke Jalingo.

Umar ya ce an umurci mutanen da suka raka shi da su fice nan take, yayin da aka tsare Boɗejo.

“A halin yanzu, ba mu san inda aka kai shi ba,” inji shi.

Ya ƙara da cewa, “Jami’an tsaron da suka raka shi tare da ba shi kariya daga Abuja zuwa Jalingo su ne daga baya suka kama shi.

“Har yanzu ba a sanar da mu dalilin kama shi ba, kuma babbar damuwar mu yanzu ita c e ba mu san inda ake tsare da shi ba.”

Kafin a kama shi, Boɗejo ya shaida wa ’yan jarida a sakatariyar APC cewa ya sayi fom ɗin tsayawa takarar sanata kuma ba zai janye wa kowane ɗan takara ba.

Ya jaddada cewa yana nan daram a takarar kuma ba zai miƙa wuya ga matsin lambar da ake masa na janye takarar sa ba.

“Na shiga wannan takara ne domin in yi nasara, kuma babu wanda zai tilasta mini na janye,” inji shi.

Har ila yau, ɗan takarar ya bayyana cewa kwamitin maslaha da ake cewa Gwamna Agbu Kefas ya kafa domin tattaunawa da ’yan takara a yankunan sanatoci uku na jihar bai tuntuɓe shi ba.

“Kwamitin maslahar da gwamnan ya kafa bai tuntuɓe ni ba, kuma ina so in bayyana a sarari cewa ba zan janye wa kowa ba, ko da kuwa akwai matsin lamba,” inji Boɗejo.

Wannan ba shi ne karo na farko da aka kama shi ba.

A 2024, jami’an Hukumar Tsaro ta DSS sun taɓa kama shi bisa zargin kafa ƙungiyar sintiri a Jihar Nasarawa.

An kama shi a hedikwatar Miyetti Allah Kautal Hore da ke Kasuwar Shanu ta Tudun Maliya, Kilomita 22, kan hanyar Abuja zuwa Keffi, Tudun Wada, Ƙaramar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa.

An ce jami’an DSS tare da wasu sojojin rundunar sojin Nijeriya sun mamaye hedikwatar Miyetti Allah da misalin ƙarfe 3:40 na yamma, sannan suka tafi da shi bayan sun kama shi a ƙofar shiga.

Har yanzu ba a san ko wannan sabon kamen yana da alaƙa da siyasa ko kuma batun tsaro ba.

Tags: APCBello BoɗejoDSSGwamna Agbu KefasJalingoMiyetti Allah Kautal HoretakaraTarabatsaro
Previous Post

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

Next Post

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!