• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da taraktoci 2,000 domin noma hekta miliyan 1.5

Wakilin Mu by Wakilin Mu
February 17, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da taraktoci 2,000 domin noma hekta miliyan 1.5
Shugaban Ƙasa Tinubu a kan tarakta

Shugaban Ƙasa Tinubu a kan tarakta

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wasu sababbin taraktocin noma guda 2,000 domin bunƙasa aikin noma na zamani a fadin kasar nan, tare da manufar noma sama da hekta miliyan 1.5 a duk shekara.

Ministan Noma da Samar da Abinci, Abubakar Kyari, shi ne ya bayyana hakan yayin bikin ƙaddamar da shirin a ranar Litinin a Abuja, inda ya ce wannan mataki wani gagarumin sauyi ne a ɓangaren noma ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cewar sa, an ƙaddamar da shirin ne a ƙarƙashin shirin Gwamnatin Tarayya na Renewed Hope National Agricultural Mechanisation Programme, wanda zai samar da taraktoci masu ƙarfin aiki tare da na’urorin noma sama da 9,000 domin inganta yawan amfanin gona.

Ya bayyana cewa za a fara da tura taraktoci 600 a mataki na farko, sannan a biyo da wasu 750 da kuma 650 a matakai na gaba har a kai ga cika adadin 2,000 a fadin ƙasar nan baki ɗaya.

Ministan ya ƙara da cewa ba za a bai wa mutane taraktocin a matsayin mallaka kai tsaye ba, sai dai za a mika su ga masu samar da ayyukan injinan noma (Mechanisation Service Providers), inda kowace na’ura za ta iya noma kusan hekta 600 a shekara.

Ana sa ran shirin zai taimaka wa manoma sama da miliyan 1.2 a duk faɗin Nijeriya, tare da inganta samar da abinci da kuma bunƙasa tattalin arzikin karkara.

Haka zalika, ya ce gwamnatin ta samar da asusun tallafin noma na Niira biliyan 50 ta hannun Bankin Masana’antu domin sauƙaƙa harkokin zuba jari a fannin noma, yayin da aka kuma tanadi Naira biliyan 250 domin tallafa wa ƙananan manoma miliyan ɗaya a daminar shekarar 2026.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta shirya samar da motocin gyaran taraktoci guda 36, da kuma gina cibiyoyin kula da injinan noma guda bakwai a sassan ƙasar nan, tare da shirin kafa babbar masana’antar haɗa taraktoci da za ta riƙa samar da tsakanin guda 2,000 zuwa 4,000 a duk shekara.

Gwamnatin ta bayyana cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da ayyukan yi, rage wahalar aikin noma, da kuma kara yawan amfanin gona domin tabbatar da wadatar abinci a ƙasar nan.

Tags: nomataraktoci
Previous Post

Tinubu ya naɗa Gwamna Uba Sani a matsayin Jakadan ‘Renewed Hope’ kuma Mataimakin Darakta-Janar

Next Post

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!