Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya rubuta takarda zuwa ga Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu, yana neman ƙarin bayani kan rahotannin da ke cewa wai Ofishin NSA ɗin (ONSA) ya sayo kimanin kilo 10 na thallium sulphate, wani sinadari mai matuƙar guba.
A cikin wasiƙar mai taken “Neman Ƙarin Bayani kan Sayo Thallium Sulphate,” El-Rufai ya ce yana ɗaukar matakin ne a matsayin sa na ɗan kasa mai kishin ƙasa, domin neman gaskiya da tabbatar da tsaro dangane da bayanan da ya bayyana a matsayin masu matuƙar muhimmanci da haɗari.
A cewar sa, bayanan da ke hannun wasu shugabannin adawa na siyasa sun nuna cewa an yi zargin sayen sinadarin ne daga wani mai samarwa a ƙasar Poland.
Ya ce: “Saboda gishirin thallium sinadarai ne masu tsananin guba kuma ana kula da su da tsauraran matakai, na yi imanin yana da muhimmanci domin kare lafiyar jama’a, tabbatar da dimokiradiyya, da kuma kiyaye amincewar jama’a a fayyace wasu bayanai.”
Ya lissafo muhimman batutuwa shida da ya nemi a yi masa ƙarin haske a kan su:
- Manufar shigo da thallium sulphate da yadda za a yi amfani da shi.
- Sunan mai samar da sinadarin da kuma ko an shigo da shi ne bisa wani izinin sinadarai ko na tsaro da ake da shi a baya.
- Jimillar adadin sinadarin da aka sayo da kuma irin yanayin sa ko ƙarfin sa.
- Hanyoyin ajiyewa da tsaron sinadarin bayan ya iso.
- Kulawar hukumomi da haɗin gwiwa da cibiyoyi masu alhakin kula da lafiyar jama’a da muhalli, ciki har da NAFDAC, NCDC, da sauran hukumomi.
- Ko an gudanar da kimanta haɗarin lafiyar jama’a ko shirye-shiryen rage haɗari, idan an yi la’akari da tsananin gubar sinadarin.
El-Rufai ya jaddada cewa tambayoyin sa sun fito ne “da kyakkyawar niyya,” kuma manufar sa ita ce tabbatar da bin doka, ƙa’idojin tsaro, da kuma fayyace gaskiya.
Ya ce: “Amintuwar jama’a da sahihancin cibiyoyin ƙasa na ƙara ƙarfi ne idan aka fuskanci duk wata barazana a buɗe kuma aka sarrafa ta yadda ya dace.”
Wannan al’amarin ya zo ne a daidai lokacin da ake fuskantar ƙarin taƙaddama ta siyasa tsakanin El-Rufai da gwamnati mai ci yanzu.
Idan kun tuna, a wata hira da ya yi da gidan talbijin na Arise, El-Rufai ya zargi Ribaɗu da kitsa wani yunƙuri na kama shi a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.
Ya ce an sanar da shi wannan zargin ne bayan wata majiya da bai bayyana ba ta ce an yi kutse an saurari wayar Ribaɗu a asirce.
Ya ce: “Gwamnati tana tunanin ita kaɗai ce ke sauraron kiran wayar mutane, amma mu ma muna da hanyoyin mu. Ya yi kiran ya ba da umarni. Wani ya saurari wayar sa. Gwamnati tana sauraron kiran mu ba tare da umurnin kotu ba. Wani ya saurari wayar sa ya gaya mana cewa ya ba da umurnin.”
Waɗannan kalamai sun haifar da muhawara a bainar jama’a kan yadda ake sa ido kan sadarwa, harkokin tsaro na ƙasa, da iyakar ikon ɓangaren zartarwa.
Tsohon gwamnan, wanda ya sha zargin gwamnatin da yi masa farautar siyasa, ya kuma ce zai amsa gayyatar da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta yi masa.
Rahotanni sun nuna cewa an aike masa da gayyatar ne yayin da yake ƙasar waje, kuma ya ce zai bayyana a gaban hukumar a gobe Litinin.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ofishin Ribaɗu dai ba su fitar da wata sanarwa kan wasiƙar ta El-Rufai ba.







