• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Ilimi

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 24, 2026
in Ilimi
A A
0
Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista
Daga hagu: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, yana musabaha da Shugaban Jami'ar Yakubu Gowon, Farfesa Hakeem Babatunde Fawehinmi, a lokacin ziyarar a ranar 22 ga Janairu, 2026, a Abuja. Hoto daga: Khalid Ahmed

Daga hagu: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, yana musabaha da Shugaban Jami'ar Yakubu Gowon, Farfesa Hakeem Babatunde Fawehinmi, a lokacin ziyarar a ranar 22 ga Janairu, 2026, a Abuja. Hoto daga: Khalid Ahmed

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa gyare-gyaren da Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake aiwatarwa a fannin ilimi sun riga sun fara samar da damarmaki na gaske ga matasan Nijeriya, tare da tabbatar da samun ilimi, daidaito da kuma inganci a jami’o’in ƙasar nan.

Ministan ya bayyana hakan ne a Abuja yayin da yake karɓar baƙuncin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon da ke Abuja (wadda aka sani da Jami’ar Abuja), Farfesa Hakeem Babatunde Fawehinmi, wanda ya jagoranci manyan jami’an jami’ar zuwa ziyarar ban-girma a ofishin sa.

A cewar Ministan, “Shirye-shirye irin su Asusun Ba da Rance ga Ɗaliban Nijeriya (NELFUND), tallafin ƙirƙire-ƙirƙire ga ɗalibai, da kuma inganta dangantaka tsakanin gwamnati da jami’o’i, sun riga sun fara ƙarfafa fannin ilimi tare da samar da damarmaki na gaske ga matasan Nijeriya.”

Ya ƙara da cewa: “A ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Gwamnatin Tarayya tana aiwatar da muhimman gyare-gyare a fannin ilimi domin tabbatar da samun ilimi, daidaito, da inganci a dukkan jami’o’in mu.”

Ministan ya kuma jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa haɗin gwiwa da jami’o’in Nijeriya, musamman wajen bunƙasa ilimin kafofin watsa labarai, haɓaka aikin jarida nagari, da kuma tunkarar ƙalubalen yaɗa labaran ƙarya da rashin amfani da fasahar zamani yadda ya dace.

Ya bayyana ziyarar a matsayin mai muhimmanci kuma mai ma’ana a wannan lokaci, yana mai cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai cibiya ce da aka sadaukar domin yi wa jama’a hidima wadda ta himmatu wajen tallafa wa cibiyoyin ilimi ta hanyar bayyana su, sadarwa da jama’a, jagoranci, da kuma daidaita manufofi.

Ya tabbatar wa tawagar jami’ar cewa a shirye Ma’aikatar take don ci gaba da haɗin gwiwa da haɗaka mai ɗorewa.

Ministan ya jinjina wa Jami’ar Yakubu Gowon bisa kafa Sashen Nazarin Kafofin Watsa Labarai da Sadarwa, yana mai bayyana rarrabe karatun Mass Communication zuwa fannoni na musamman a matsayin abin da ya dace da tsarin duniya.

Ya jaddada buƙatar ƙarin hulɗa tsakanin ƙwararrun ’yan jarida da ɗalibai domin cike giɓin da ke tsakanin karatun aji da aikace-aikacen zahiri.

Ya kuma bayyana jagorancin Gwamnatin Tarayya wajen bunƙasa ilimin kafofin yaɗa labarai da bayanai, inda ya ambaci yadda Nijeriya ta karɓi baƙuncin Cibiyar UNESCO ta Ilimin Kafofin Watsa Labarai (IMILI)–wadda ita ce irin ta ta farko a duniya—a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin yaƙi da labaran ƙarya da ƙarfafa amincewar jama’a ga labaran da suke samu.

Tun da farko, Shugaban jami’ar, Farfesa Fawehinmi, ya taya Ministan murna bisa jagorancin sa a fannin yaɗa labarai, sannan ya nemi goyon baya, haɗin gwiwa, da jagoranci daga Ma’aikatar ga Sashen Nazarin Kafofin Watsa Labarai da Sadarwa gabanin tantance shi.

Ya kuma bayyana shirye-shiryen jami’ar na mara wa shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya da manufofin ta baya.

Tags: HakeemBabatundeFawehinmiJami'arAbujaJami'arYakubuGowonMohammedIdrisyaɗalabarai
Previous Post

CBN zai fito da tsarin magance yawan samun matsalolin kati da na’urar ATM

Next Post

Yadda shirin CBN na ƙarfafa jarin bankuna zai fara samar da gagarumin tattalin arziki tun daga 2026

Related Posts

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya
Ilimi

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

April 26, 2026
NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795
Ilimi

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795

April 19, 2026
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi
Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

March 15, 2026
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ilimi

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

February 18, 2026
Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano
Ilimi

Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano

January 20, 2026
Gwamnatin Tarayya ta buɗe rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na PTDF
Ilimi

Gwamnatin Tarayya ta buɗe rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na PTDF

January 20, 2026
Next Post
Kamfanonin ‘yan canji 82 kaɗai CBN ya ba lasin canjin kuɗin ƙasashen waje

Yadda shirin CBN na ƙarfafa jarin bankuna zai fara samar da gagarumin tattalin arziki tun daga 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!