• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Siyasa

Duk za a fice daga ADC idan Atiku ya zama ɗan takarar jam’iyyar, inji Hakeem Baba-Ahmed

ALI KANO by ALI KANO
January 20, 2026
in Siyasa
A A
0
Duk za a fice daga ADC idan Atiku ya zama ɗan takarar jam’iyyar, inji Hakeem Baba-Ahmed
Alhaji Hakeem Baba-Ahmed

Alhaji Hakeem Baba-Ahmed

Hakeem Baba-Ahmed, tsohon mai ba wa Mataimakin Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin siyasa, ya ce jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) na iya fuskantar rugujewar cikin gida idan har Atiku Abubakar ya fito a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027.

Baba-Ahmed ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin wata hira a shirin Politics Today da ake watsawa a tashar talbijin ta Channels.

Ya ce Atiku yana da kyakkyawan matsayi na samun tikitin ADC idan jam’iyyar ta gudanar da babban taron ta na ƙasa.

“Idan ADC ta je taron ƙasa, kuma tabbas za ta je domin shi ne abin da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku ke so, zai samu tikitin,” inji Baba-Ahmed.

“Sannan mutane da yawa za su fice, domin mutane da dama da ke cikin jam’iyyar suna can ne saboda abu ɗaya—su ma suna son tikitin.”

Ya ce a halin yanzu ADC na ɗauke da manyan ’yan siyasa masu suna, kuma burikan su za su yi karo da juna yayin zaɓen ɗan takara.

Baba-Ahmed ya ƙara da cewa daidaiton cikin jam’iyyar na iya ƙara yin rauni sakamakon muradin Peter Obi, tsohon gwamnan Jihar Anambra.

“Ɗaya daga cikin dalilan da Peter Obi ke cewa, ‘Ku dubi ni, ba na nan don lamba biyu, ba na nan don taron ƙasa, na zo ne don ɗaga tutar jam’iyya,’ shi ne yana da mutane da tun farko suna yi masa maganganu a hankali,” inji shi.

“Amma yanzu suna cewa, ‘Ka shiga layi. Ba kai kaɗai ne ke da buri a nan ba.’”

Tsohon mai ba da shawarar siyasar ya ce Obi ya fi sabawa da a zaɓe shi ta hanyar yarjejeniya (consensus) fiye da shiga zaɓen fidda gwani mai tsauri.

“Peter Obi ba ya yin taron ƙasa. Kawai yana zuwa ne a naɗa shi,” inji shi.

“Don haka, ADC za ta yi asarar membobi bayan taron ta na ƙasa, domin kusan tabbas tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku ne zai lashe tikitin, kuma idan hakan ta faru, wasu za su fice, jam’iyyar kuma za ta lalace ƙwarai.”

Tags: ADCAtikuAbubakarHakeemBabaAhmedPeterObiZaɓen2027
Previous Post

Muhimman Shawarwarin Tsaro Ga Magidanta Da Iyalai

Next Post

Shirin ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan ɗaya: Bankuna 21 da suka cika ƙa’idojin CBN

Related Posts

An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano
Siyasa

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano

May 5, 2026
Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Shirin ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan ɗaya: Bankuna 21 da suka cika ƙa’idojin CBN

Shirin ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan ɗaya: Bankuna 21 da suka cika ƙa'idojin CBN

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!