Ɗaya daga cikin waɗanda Hukumar Tsaro ta Farar Hula (DSS) ta gurfanar tare da Khalid Al-Barnawi da wasu mutum uku bisa zargin hannu a harin bam na ranar 26 ga Agusta, 2011, da aka kai wa ginin Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) a Abuja, ya bayyana wa Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja yadda ya shiga ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram.
A zaman shari’ar da aka ci gaba da yi yau Laraba kan Al-Barnawi da wasu mutum huɗu, wanda ake tuhuma na biyu, Mohammed Bashir Saleh, a cikin wani bidiyon da aka kunna a gaban kotu, ya ce ya haɗu da Al-Barnawi ne a Bauchi jim kaɗan kafin harin ginin MDD ɗin, kuma daga wannan lokaci alaƙar da ke tsakanin su ta ƙarfafa har ta kai shi shiga Boko Haram.
Hukumar DSS ta kama Al-Barnawi ne a watan Afrilun 2016 a Lokoja, Jihar Kogi, shekaru biyar bayan harin bam ɗin da aka kai ginin MDD a Abuja — wanda shi ne harin farko irin sa da aka taɓa kai wa dukiyar wata hukumar ƙasa da ƙasa a Nijeriya — wanda ya yi sanadin mutuwar fiye da mutane 20 tare da jikkata sama da 70.
Al-Barnawi, wanda kuma ake kira da sunaye daban-daban kamar Kafuri/Naziru/Alhaji Yahaya/Mallam Dauda/Alhaji Tanimu, DSS ta gurfanar da shi ne tare da Mohammed Bashir Saleh; Umar Mohammed Bello wanda aka fi sani da Datti; Mohammed Salisu; da Yakubu Nuhu wanda aka fi sani da Bello Maishayi.
A zaman shari’ar ranar Laraba, kotu ta kalli wani bidiyo na ƙarin zaman tambayoyi da aka yi da Saleh, sannan aka fara yi wa shaidar tuhuma ta uku tambayoyi a ci gaba da shari’a cikin shari’a (“trial-within-trial”) da ake gudanarwa domin tantance ko bayanan furucin da ake zargin waɗanda ake tuhuma sun bayar sun kasance na son rai ne ko akasin haka.
A yayin yi masa tambayoyi ta bakin lauyan wanda ake tuhuma na farko (Al-Barnawi), F.K. Kaigama, shaidar da aka bayyana da suna “TSR3” ta ce yana aiki a Sashen Fasaha na DSS, kuma daga cikin ayyukan sa akwai girka na’urorin ɗaukar sauti da bidiyo a ɗakin tambayoyi.
Shaidar ta ƙara da cewa yana ɗaukar sauti da bidiyo na waɗanda ake zargi a lokacin zaman tambayoyi.
Da aka tambaye shi sauran ayyukan sa, ya ce: “Baya ga waɗannan ayyuka, ina kuma gudanar da binciken na’urar kwamfuta (computer forensics), binciken wayoyin salula, binciken wurin aikata laifi kamar tattara hoton yatsu (fingerprints) daga wurin laifi da kuma nazarin su a ɗakin gwaje-gwaje.”
Shaidar ta ce ba wai kawai ya girka na’urar ɗaukar sauti da bidiyo ba dangane da wanda ake tuhuma na farko; ya ƙara da cewa shi ne ya ɗauki sauti da bidiyon zaman tambayoyin da aka yi wa wanda ake tuhuma na farko kai-tsaye yayin da suke faruwa.
Ya ce abu na uku da ya yi dangane da wanda ake tuhuma na farko shi ne ɗaukar sauti da bidiyon zaman karɓar bayani, da kuma ɗaukar sauti da bidiyon fassarar bayanan da wanda ake tuhuma na farko ya bayar.
Da aka tambaye shi ko akwai wani mutum mai suna James a Sashen Fasaha inda yake aiki, shaidar ta ce akwai James da dama a Sashen Fasaha na DSS.
A wannan mataki, Mai Shari’a Emeka Nwite ya bayar da umurnin ɗage ci gaba da shari’ar bisa dalilin cewa yana da wasu ayyuka a gaban sa.
Bisa amincewar lauyoyin ɓangarorin da ke shari’ar, Mai Shari’a Nwite ya ɗage shari’ar zuwa ranar 2 ga Maris domin ci gaba da yi wa shaidar tuhuma ta uku (PW3) tambayoyi a shari’ar “trial-within-trial”.







