Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, a ranar Talata ya fara zama a aji don karɓar darussa a matsayin sa na ɗalibi a Jami’ar Northwest da ke Kano, inda yake karanta fannin Shari’a a mataki na 200.
Khalifa Sanusi II ya shiga cikin aji ne tun da sassafe tare da sauran abokan karatun sa, yana sanye da doguwar riga baƙa da rawani fari. Ya zauna a bayan aji cikin kujerar mutane uku yayin darasin.
Shiga ajin a karon farko da Sarkin ya yi ya zo ne bayan ya kammala dukkan matakan rajista bisa ƙa’idojin jami’ar.
Jami’ar ta ba shi damar shiga karatu ne a makon da ya gabata, tana la’akari da ƙwarewar sa mai yawa a fannonin shugabanci, tattalin arziki da hidimar jama’a.
Sanusi II dai yana da digirin digirgir (PhD), kuma tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya ne, wanda ya ci gaba da taka muhimmiyar rawa a harkokin jama’a, ana girmama shi saboda ƙwarewar sa tare da shaharar sa wajen fafutukar inganta ilimi da ƙarfafa wa matasa gwiwa.
Ɗalibai ‘yan ajin sa waɗanda sun fi shi ƙarancin shekaru sun bayyana farin cikin su da ya shigo harabar jami’ar, suna jaddada cewa hakan na da muhimmanci domin yana nuna tasirin Sarkin da a rayuwar jami’a kai-tsaye.
Idan kun tuna, a ranar 15 ga Janairu, 2026 mun ba ku labarin cewa Sarkin ya samu shiga jami’ar domin karatun Shari’ar Musulunci da Shari’ar Bature a matakin digirin farko.







