Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa ɓangaren Nijeriya na Kwamitin Aiki na Haɗin Gwiwar Amurka da Nijeriya, a matsayin wani mataki na zurfafa haɗin kai wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.
Wata sanarwa da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Mista Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, ta ce tsarin kwamitin aiki na haɗin gwiwar yana daga cikin yarjejeniyar da aka cimma yayin ziyarar da wata tawaga ta manyan jami’an gwamnati daga Nijeriya, ƙarƙashin jagorancin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, suka kai Washington, DC, kwanan nan.
Ribadu zai jagoranci ɓangaren Nijeriya na kwamitin aikin, tare da goyon bayan tawagar manyan jami’ai daga hukumomi daban-daban da abin ya shafa.
Membobin kwamitin sun haɗa da Ministan Harkokin Waje, Jakada Yusuf Maitama Tuggar; Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar; Ministan Cikin Gida, Hon. Olubunmi Tunji-Ojo; Ministan Harkokin Jinƙai, Dr Bernard M. Doro; Shugaban Ma’aikatan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Darakta-Janar na Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA), Jakada Mohammed Mohammed; da Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Mista Kayode Egbetokun.
Miss Idayat Hassan daga Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA) da Mista Paul Alabi daga Ofishin Jakadancin Nijeriya a Amurka za su yi aiki a matsayin sakatariya.
Tinubu ya shawarci membobin kwamitin da su yi aiki tuƙuru tare da takwarorin su na Amurka don tabbatar da ingantacciyar aiwatar da duk yarjejeniyoyi a fannoni daban-daban.







