Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya aike da saƙon godiya ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan kwangilolin ayyuka daban-daban da Gwamnatin Tarayya ta bayar a Jihar Kaduna, yana mai cewa za su “sauya yanayin tattalin arziki da zamantakewa na jihar gaba ɗaya.”
A cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar a wannan Juma’a, gwamnan ya lissafa manyan ayyukan da suka haɗa da aikin ƙaramar hanyar dogo a garin Kaduna, wanda wani babban aiki ne mai tsawon kilomita 30 daga garin Rigachikun zuwa Sabon Tasha cikin Kaduna, tare da wani layi mai tsawon kilomita 20 daga unguwar Millennium City zuwa Rigasa, wanda gaba ɗaya ya zama hanyar sufuri ta cikin birni mai tsawon kilomita 50, da kimanin kuɗin sa ya kai Naira tiriliyan 1.
Wani muhimmin aikin kuma shi ne sake gina hanyar Mando a Kaduna zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122, wanda kuɗin sa ya kai Naira biliyan 178.
“Gaba ɗaya, waɗannan ayyuka ba wai saka jari kawai ba ne a fannin gine-ginen ababen more rayuwa, har ma suna wakiltar sabon tsarin inganta zirga-zirga, tsaro da ƙarfafa tattalin arziki a duk faɗin Jihar Kaduna,” inji shi.
Gwamnan ya lura da cewa goyon bayan da Gwamnatin Tarayya ta bayar ga aikin ƙaramin layin dogo “abin tarihi ne kuma zai haifar da gagarumin sauyi,” yana mai cewa, “Wannan yana ƙarfafa hangen nesan mu na tsarin sufuri mai haɗin kai, wanda ya dogara da tsarin Bus Rapid Transit mai tsawon kilomita 24 da ake aiwatarwa a halin yanzu.”
“Kaduna ta taka rawar gani a Arewacin Nijeriya ta hanyar ƙirƙirar cikakkiyar Manufar Sufuri ta Jiha, wadda ta mayar da hankali kan inganci, tsaro, kare muhalli da kuma sauƙin farashi.
“Ta hanyar shirye-shirye irin su samar da motocin bas-bas masu amfani da iskar gas (CNG) masu farashi mai rahusa, tashoshin zamani, da hanyoyin sufuri da aka tsara yadda ya kamata, muna sanya Kaduna ta zama cibiyar sufuri da harkokin jigilar kayayyaki a nan gaba.
“Kasancewar an zaɓi Kaduna ta jagoranci wannan sauyi, tare da zama jiha ta biyu a ƙasar nan wadda za ta fara cin moriyar tsarin ƙaramin layin dogo, yana nuna irin amincewar da aka yi da hangen nesan mu da kuma ƙwarewar mu wajen aiwatarwa.
“Wannan shaida ce ta irin salon shugabanci a matakin ƙasa wanda ke gane ƙwarewa, yana ba da lada ga shiri, kuma yana inganta cigaba ba tare da son kai ba.”
Game da aikin gyaran hanyar Mando zuwa Birnin Gwari kuwa, wanda ke da muhimmanci ta fuskar alama da amfani, gwamnan ya ce: “Ina tuna ziyarar da Mai Girma Shugaban Ƙasa ya kai Birnin Gwari kafin zaɓen 2023, a lokacin da yankin ke fama da rashin tsaro da rashin kulawar ababen more rayuwa. Alƙawarin da ya yi a lokacin ya kasance bayyananne.
“A yau, ana cika wannan alƙawari. Wannan hanya ba kawai za ta inganta haɗin kai ba, har ma za ta ƙarfafa tsaro, ta sauƙaƙa aikin noma, kuma ta dawo da ƙwarin gwiwa ga al’ummomin da suka daɗe suna fama da wariya.”
A cewar gwamnan, “Jihar Kaduna tana ci gaba da jajircewa wajen aiwatar da waɗannan ayyuka yadda ya kamata. Muna kallon su ba a matsayin ayyuka na ɗan lokaci ba, sai dai a matsayin ginshiƙai na dindindin da za a gina makoma mai wadata, tsaro da haɗin kai a kan su.
“Muna gode wa Mai Girma Shugaban Ƙasa bisa jajircewar sa ga Jihar Kaduna da kuma cigaban ƙasar mu cikin adalci.”







