Tsohon Shugaban Sashen Koyon Aikin Jarida (Mass Communication) na Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna (Kaduna Polytechnic), Dakta Bashir Hadi Ashara, ya rasu.
Ya rasu ne a daren jiya Alhamis, inda ya bar tarihi na hidima ga fannin ilimi da aikin jarida.
Za a gudanar da sallar jana’izar sa a yau a Masallacin Ɗanfodiyo da ke Unguwar Sanusi a Kaduna.
Ashara ƙwararren ɗan jarida ne da ya yi aiki da kamfanin jaridun New Nigerian da kuma tsohon kamfanin Nationhouse Press, inda ya bayar da gudunmawa ga mujallar The Sentinel da jaridar Nasiha.
Abokan aikin sa na tuna shi a matsayin mutum mai tawali’u kuma ginshiƙi a cikin al’ummar kafafen yaɗa labarai.
A cikin wani rubutu da aka wallafa a Facebook domin ba da sanarwar rasuwar sa, wani na kusa da shi ya bayyana wata ƙaramar nadama: Ashara ya aiko da saƙon gaisuwa mai daɗi a yammacin Laraba, amma wanda aka tura wa saƙon bai sani ba domin yana jagorantar wani taron horaswa da Ƙungiyar Matan ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NAWOJ) ta shirya a Zariya, don haka bai samu damar mayar da martani ba. Wannan rubutun ya zama tunatarwa mai taɓa zuciya game da raunin rayuwa.
Ashara ya horar da ɗimbin matasa a lokacin da yake shugabantar Sashen Koyon Aikin Jarida a Kaduna Polytechnic.
Abokai da tsofaffin ɗaliban sa sun yi ta bayyana alhinin su a soshiyal midiya kan rasuwar wannan mutum da aka bayyana a matsayin fitaccen malami kuma nagari.
Allah ya gafarta masa kurakuran sa, ya saka masa da alherin hidimar sa ga ilimi, ya kuma ba shi Aljannar Firdausi, amin.







