• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Siyasa

Tinubu yana murɗe wuyan dimokiraɗiyya — Nijeriya na gangarawa zuwa mulkin kama-karya – Atiku

ALI KANO by ALI KANO
March 23, 2026
in Siyasa
A A
0
Ba cewa na yi na daina takara ba, inji Atiku kan hirar sa da BBC Hausa
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma fitaccen jigo a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya yi gargaɗi mai tsanani cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana rushe dimokiraɗiyya a zahiri tare da tura Nijeriya zuwa cikakken mulkin kama-karya, lamarin da ke da haɗari ga duk yankin Afrika ta Yamma.

A wata kakkausar suka da ya yi a ranar Litinin, Atiku ya mayar da martani kan abin da ya bayyana a matsayin ƙawanya da jami’an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) suka yi wa gidaje da harkokin kasuwancin tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami—matakin da ya kira rashin bin doka, na ramuwar gayya, kuma na siyasa.

A sanarwar da ofishin sa na yaɗa labarai suka fitar, Atiku ya ce jami’an DSS sun mamaye tare da kulle kadarorin Malami jim kaɗan bayan ziyarar sa—duk da cewa batun yana gaban kotu.

Ya ce: “Wannan ba shugabanci ba ne. Wannan tsoratarwa ce. Wannan gwamnati ce da ke amfani da ikon hukuma don murƙushe masu adawa.”

Atiku ya yi gargaɗin cewa Nijeriya tana fuskantar rushewar ƙa’idojin dimokiraɗiyya cikin sauri a ƙarƙashin Tinubu, inda cibiyoyin gwamnati suka koma kayan aikin tsangwama na siyasa.

“Abin da muke gani shi ne bayyanannen cin zarafin iko—ana amfani da hukumomin tsaro ba don kare ƙasa ba, sai don biyan buƙatun siyasa. Ta haka ne dimokiraɗiyya ke mutuwa,” inji shi.
Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da gudanar da wani tsari na musamman domin murƙushe muryoyin adawa tare da kafa cikakken iko na siyasa gabanin zaɓen 2027.

“A fayyace a sarari: wannan gwamnati tana tsoron fafatawa. Shi ya sa take komawa amfani da ƙarfi—tsangwama, tsoratarwa, da ƙoƙarin karya gwiwar shugabannin adawa har su miƙa wuya,” inji shi.

Ya ƙara da cewa ci gaba da tsananta wa mutane irin su Nasir El-Rufa’i da Abubakar Malami wani ɓangare ne na wata babbar manufa ta tilasta musu barin siyasar adawa su koma sahun jam’iyya mai mulki ta APC.

“Wannan cin zarafin siyasa ne a mafi girman matsayi—ko ku zo mu tafi tare ko a lalata ku. Wannan ne saƙon da ake aikawa,” inji Atiku.

Tags: adawaADCAtikuAbubakarDSSEl-RufaiMalamiTinubu
Previous Post

Shettima ya karɓi gwamnan Adamawa cikin APC, ya ce jam’iyyar ta nuna siyasar cigaba a ƙarƙashin Tinubu

Next Post

Kafafen yaɗa labarai babban makami ne na isar da saƙo da shafar tunanin al’umma kan alƙibla – Idris

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Rikicin shugabanci a ADC: Ɓangaren David Mark ya rubuta wa CJN takarda, ya roƙi a gaggauta yanke hukunci
Siyasa

Rikicin shugabanci a ADC: Ɓangaren David Mark ya rubuta wa CJN takarda, ya roƙi a gaggauta yanke hukunci

April 28, 2026
A taron Ibadan, ‘yan adawa sun haɗa kai, sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya a zaɓen 2027
Siyasa

A taron Ibadan, ‘yan adawa sun haɗa kai, sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya a zaɓen 2027

April 25, 2026
Next Post
Kafafen yaɗa labarai babban makami ne na isar da saƙo da shafar tunanin al’umma kan alƙibla – Idris

Kafafen yaɗa labarai babban makami ne na isar da saƙo da shafar tunanin al'umma kan alƙibla - Idris

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!