• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS) ya buƙaci sojojin Nijeriya su mutunta haƙƙin ɗan’adam da tsaron jama’a

Admin-content by Admin-content
March 17, 2026
in Tsaro
A A
0
Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS) ya buƙaci sojojin Nijeriya su mutunta haƙƙin ɗan’adam da tsaron jama’a
Hagu zuwa dama: Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, tare da Kwamandan Kwalejin Yaƙin Sojojin Nijeriya, Manjo Janar Umar Alkali, a wajen taron yau a Abuja.

Hagu zuwa dama: Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, tare da Kwamandan Kwalejin Yaƙin Sojojin Nijeriya, Manjo Janar Umar Alkali, a wajen taron yau a Abuja.

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umurci kwamandoji a dukkan matakai da su kiyaye muhimman haƙƙin ɗan’adam da kuma tsaron dukkan ’yan Nijeriya yayin gudanar da ayyukan su na kundin tsarin mulki, yana mai jaddada cewa mutunta haƙƙin ɗan’adam yana da matuƙar muhimmanci ga nasarar ayyuka da kuma daidaiton ƙasa.

Muƙaddashiyar Daraktan Hulɗa da Jama’a na Sojoji, Kanar Appolonia Anele, ta bayyana a cikin wata sanarwar manema labarai cewa COAS ya bayar da wannan umurnin ne a yau Talata, 17 ga Maris, 2026, yayin da yake gabatar da lacca kan falsafar jagorancin sa ga mahalarta Kwasa-kwasan Kwalejin Dabarun Yaƙi ta Nijeriya 10/2026 a Abuja.

Shaibu ya bayyana cewa falsafar jagorancin sa mai taken, “Inganta sauyin Sojojin Nijeriya zuwa rundunar da ta fi dacewa, shirin yaƙi, kuma mai juriya wadda za ta iya cika nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata cikin haɗin gwiwar hukumomi daban-daban,” ita ce ginshiƙin da ra’ayin sa na jagoranci ya ta’allaƙa kai.

Ya jaddada cewa bin dokokin jinƙai na ƙasa da ƙasa, ka’idojin gudanar da aiki (Rules of Engagement), da sauran tsare-tsare da aka kafa yayin gudanar da ayyuka, ba wai kawai yana kare fararen hula ba ne, har ma yana ƙara amincewar jama’a da kuma tallafa wa ayyukan da suka dogara da bayanan sirri.

Wani sashe na mahalartan taron

COAS ya ce tsawon shekaru, sojojin Nijeriya sun ƙirƙiri dabaru daban-daban da suka tsara yadda suke tunkarar ƙalubalen tsaro da ke sauyi a ƙasar.

Ya kuma jaddada wa mahalarta su rungumi falsafar jagorancin sa, wadda ta ta’allaƙa kan manufar “Soja a Farko” (Soldier First Concept), wadda ke ba da fifiko ga jin daɗin ma’aikata.

Ya bayyana cewa wannan manufa ta ginu ne kan muhimman ginshiƙai kamar ƙwarewa, ingantaccen gudanarwa, shirye-shiryen aiki, haɗin gwiwar dabaru, da jagoranci nagari, waɗanda ke da muhimmanci ga ingancin ayyuka.

Babban hafsan ya kuma shawarci mahalartan da su ba da muhimmanci ga haɓaka ƙwarewar waɗanda ke ƙarƙashin su ta hanyar horo mai tsari, inganci, kuma mai mayar da hankali kan manufa.

Ya jaddada cewa horo kan mutunta haƙƙin ɗan’adam da kare fararen hula yana da matuƙar muhimmanci, domin yana nuna ainihin ma’anar rantsuwar biyayya da dukkan jami’ai suke yi.

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, yana gabatar da jawabi a taron

Kwamandan Kwalejin Dabarun Yaƙi ta Nijeriya, Manjo Janar Umar Alkali, ya gode wa COAS ɗin bisa ci gaba da goyon bayan sa ga kwalejin.

Ya ce laccar ta yi tasiri sosai ba ga mahalarta kaɗai ba, har ma ga cibiyar gaba ɗaya.

Tags: Kwalejin Dabarun YaƙiLaftanar Janar Waidi ShaibuWar College Abuja
Previous Post

Babban jami’in yaƙi da ta’addanci na Amurka ya yi murabus kan yaƙin Iran, ya ce Iran ba ta da wata barazana ta gaggawa

Next Post

Tinubu ya umurci masu riƙe da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara su yi murabus kafin 31 ga Maris

Related Posts

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya
Tsaro

‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya

April 16, 2026
Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su
Tsaro

Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su

April 15, 2026
Nijeriya ba za ta miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba – Gwamnatin Tarayya
Tsaro

Gwamnatin Tarayya ta kare harin jirgin sama a Jilli, ta ba da umurnin bincike

April 14, 2026
An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno
Tsaro

An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno

April 13, 2026
Next Post
Tinubu ya bayyana sunayen ƙasashen da ya tura jakadu 65 a duniya

Tinubu ya umurci masu riƙe da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara su yi murabus kafin 31 ga Maris

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!