Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhinin sa game da sabon harin ta’addanci da aka kai birnin Maiduguri na Jihar Borno, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin ɗacin rai da ban-takaici.
Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, 17 ga Maris, 2026, Tinubu ya jajanta wa mutanen da suka rasa rayukan su da kuma waɗanda suka jikkata, yana mai jaddada cewa gwamnati tama tare da jama’ar Borno a wannan mawuyacin lokaci.
Shugaban ya bayyana cewa waɗannan hare-hare suna nuna alamun fargaba da matsin lamba da ’yan ta’addan ke fuskanta daga dakarun tsaron Nijeriya.
“Waɗannan ayyukan ta’addanci yunƙuri ne na ƙarshe na matsananciyar fargaba da waɗannan masu laifin suke yi domin dasa tsoro a zukatan mutane, sakamakon irin luguden wutar da suke fuskanta daga jami’an mu,” inji shi.
Tinubu ya ƙara da cewa, a taron tsaro da ya gudanar a ƙarshen makon jiya, ya amince da samar da ƙarin kayan aiki da tallafin ayyuka ga hukumomin tsaro domin ƙarfafa dabarun su na yaƙi da ta’addanci.
Domin tabbatar da an magance lamarin cikin gaggawa, Shugaban ya ba wa manyan hafsoshin tsaro na ƙasa umurnin gaggawa na su koma birnin Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro da kan su.
Haka kuma, ya umurci hukumomin agajin gaggawa da su tabbatar da sun ba duk waɗanda suka jikkata kulawar da ta dace.
A ƙarshe, ya jaddada cewa babu wani lungu a Nijeriya da zai zama wurin ɓuya ga ’yan ta’adda, inda ya ce: “Ba za mu taɓa miƙa wuya ga tsoro ba. Za mu nemo su, mu fuskance su, kuma mu murƙushe su baki ɗaya.”







