• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya naɗa Fola Adeola shugaban kwamitin kawo sababbin matakan gyara a harkar fetur

Wakilin Mu by Wakilin Mu
March 14, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Tinubu ya naɗa Fola Adeola shugaban kwamitin kawo sababbin matakan gyara a harkar fetur
Cif Fola Adeola

Cif Fola Adeola

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Cif Fola Adeola, ɗaya daga cikin waɗanda suka assasa bankin Guaranty Trust Bank (GTB), a matsayin shigaban wani kwamiti na musamman wanda zai ɓullo da sababbin matakan gyare-gyare a ɓangaren harkar fetur.

Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai, Bayo Onanuga, shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

Adeola, wanda cikakken sunan sa Tajudeen Afolabi Adeolalisten, ɗan shekara 72, memba ne a Hukumar Afrika (Commission for Africa) kuma shugaban FATE Foundation.

Sauran membobin kwamitin su ne Ademola Adeyemi-Bero, Osagie Okunbor, Abubakar Suleiman, Adaeze Aguele, Farouk Gumel, Phillipa Osakwe-Okoye da Seyi Bella, yayin da Mofoluwasho Fadayomi ne sakatare.

A cewar Onanuga, an ɗora wa kwamitin alhakin tsara matakan gyare-gyare da za su bunƙasa harkar man fetur, su jawo ƙarin zuba jari, tare da ƙara wa tattalin arzikin ƙasar nan daraja.

Kwamitin zai riƙa kai rahoto kai-tsaye ga Shugaban Ƙasa duk wata, sannan zai gabatar da rahoton wucin-gadi bayan wata uku, yayin da ake sa ran kammala rahoton ƙarshe cikin wata shida.

Ana sa ran kwamitin zai gabatar da manyan tsare-tsare uku na gyara, ciki har da matakan sauya tsarin ɓangaren nan take.

A cewar sa, shirin zai bayar da damar samun jarin dala biliyan biyar zuwa 10, da kuma wani tsari na sauya tsarin makamashi na ƙasar nan na tsawon shekaru 10.

Tags: feturFolaAdeolagyarakwamitiTinubu
Previous Post

Dalilin da ya sa na bar PDP – Tambuwal

Next Post

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!