• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Friday, May 15, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Siyasa

Dalilin da ya sa na bar PDP – Tambuwal

New Citizen Hausa by New Citizen Hausa
March 13, 2026
in Siyasa
A A
0
Dalilin da ya sa na bar PDP – Tambuwal
Sanata Aminu Tambuwal yana karɓar riga da hular ADC, lokacin ficewar sa daga PDP

Sanata Aminu Tambuwal yana karɓar riga da hular ADC, lokacin ficewar sa daga PDP

Sanata Aminu Tambuwal (ADC–Sokoto ta Kudu) ya ce ya bar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ne sakamakon rikicin da ya daɗe yana addabar jam’iyyar.

Ya bayyana rikicin a matsayin wani shiri da aka tsara domin raunana rawar da jam’iyyun adawa za su taka gabanin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Tambuwal ya yi wannan zargi ne a ranar Alhamis a Sokoto yayin da yake ganawa da manema labarai kan sauya sheƙar sa daga PDP zuwa jam’iyyar Africa Democratic Congress (ADC).

Tsohon gwamnan Jihar Sokoto ɗin ya ce matakin da ya ɗauka na barin PDP ya biyo bayan tuntuɓa mai zurfi da kuma dogon nazari kan yanayin siyasar Nijeriya.

A cewar sa, shirin sauya sheƙar ya fara tun fiye da shekaru biyu da suka gabata.

“Lokacin da muka duba makomar gaba, mun ga alamun da ke nuna cewa gwamnatin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki tana iya ƙoƙarin mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya tak,” inji shi.

Tambuwal ya bayyana cewa an kafa wani kwamiti da ya ƙunshi ƙwararrun masu nazarin siyasa, ‘yan siyasa masu aiki da kuma farfesoshi daga manyan jami’o’i domin su yi nazari kan yadda siyasar Nijeriya take sauyawa.

Ya ce kwamitin ya ƙunshi membobi daga PDP da jam’iyyar Labour Party da kuma APC.

“Daga binciken da aka yi, ya nuna cewa PDP da Labour Party, waɗanda su ne manyan jam’iyyun adawa, na iya fuskantar matsalar ci gaba da wanzuwa a yadda suke a yanzu.

“Abin da binciken ya nuna shi ne cewa jam’iyyun biyu ba za su kasance cikin wani ƙarfi da zai ba su damar tsayar da ‘yan takarar shugaban ƙasa masu ƙarfi a zaɓen gama-gari na 2027 ba,” inji shi.

Tambuwal ya yi zargin cewa ana ƙoƙarin raunana PDP da Labour Party zuwa matsayin ƙananan jam’iyyu, waɗanda a cewar sa galibi kan shiga yarjejeniya da Gwamnatin Tarayya a lokacin zaɓe.

“Wannan shi ne abin da ake son a cimma, kuma ɗaya daga cikin sharuɗɗan shi ne kada Peter Obi ya ci gaba da kasancewa a jam’iyyar Labour domin tsayawa takara,” inji shi.

A cewar sa, wannan lamari ne ya sa ‘yan siyasa masu irin wannan ra’ayi suka yanke shawarar haɗe kai da jam’iyyar ADC domin gina wani dandali mai ƙarfi na adawa.

“Mu ba sababbin shiga ba ne a wannan harkar siyasa. Mun ga alamun tun da wuri, kuma muka yanke shawarar ɗaukar mataki domin daƙile wannan yunƙuri da aka shirya,” inji shi.

Tambuwal ya ƙara da cewa yunƙurin ADC ba wai domin burin mutum ɗaya ba ne, sai dai domin gina wata jam’iyya da za ta mayar da hankali kan jama’a.

“ADC ta shafi jama’a ne kuma ta shafi Nijeriya. A yau, ƙasar nan ta kasu gida biyu: waɗanda ke cikin gwamnati da kuma waɗanda ba su cikin ta.

“Yawancin ‘yan Nijeriya ba su gamsu da halin da ake ciki ba, ciki har da matsalar tsaro, talauci, cin hanci da rashawa da kuma cin amanar amanar jama’a,” inji shi.

Ya jaddada cewa a ƙarshe jama’a ne ke yanke hukunci a zaɓe a Nijeriya, yana mai cewa shugabannin ƙasa da gwamnonin jihohi ma sun taɓa shan kaye a zaɓe idan masu kaɗa ƙuri’a ba su gamsu da jagorancin su ba.

Tambuwal ya nanata cewa sauya sheƙar sa ba domin wata buƙata ta siyasa ta kan sa ba ce, sai dai domin makomar al’ummar sa da kuma makomar Nijeriya baki ɗaya.

Tags: ADCAminuWaziriTambuwalPDPsauyasheƙazaben2027
Previous Post

Gwamnan CBN ya jaddada muhimmancin ƙarfafa cibiyoyi da gyaran jarin bankuna domin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa

Next Post

Tinubu ya naɗa Fola Adeola shugaban kwamitin kawo sababbin matakan gyara a harkar fetur

Related Posts

An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano
Siyasa

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano

May 5, 2026
Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Tinubu ya naɗa Fola Adeola shugaban kwamitin kawo sababbin matakan gyara a harkar fetur

Tinubu ya naɗa Fola Adeola shugaban kwamitin kawo sababbin matakan gyara a harkar fetur

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!