Sanata Aminu Tambuwal (ADC–Sokoto ta Kudu) ya ce ya bar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ne sakamakon rikicin da ya daɗe yana addabar jam’iyyar.
Ya bayyana rikicin a matsayin wani shiri da aka tsara domin raunana rawar da jam’iyyun adawa za su taka gabanin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Tambuwal ya yi wannan zargi ne a ranar Alhamis a Sokoto yayin da yake ganawa da manema labarai kan sauya sheƙar sa daga PDP zuwa jam’iyyar Africa Democratic Congress (ADC).
Tsohon gwamnan Jihar Sokoto ɗin ya ce matakin da ya ɗauka na barin PDP ya biyo bayan tuntuɓa mai zurfi da kuma dogon nazari kan yanayin siyasar Nijeriya.
A cewar sa, shirin sauya sheƙar ya fara tun fiye da shekaru biyu da suka gabata.
“Lokacin da muka duba makomar gaba, mun ga alamun da ke nuna cewa gwamnatin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki tana iya ƙoƙarin mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya tak,” inji shi.
Tambuwal ya bayyana cewa an kafa wani kwamiti da ya ƙunshi ƙwararrun masu nazarin siyasa, ‘yan siyasa masu aiki da kuma farfesoshi daga manyan jami’o’i domin su yi nazari kan yadda siyasar Nijeriya take sauyawa.
Ya ce kwamitin ya ƙunshi membobi daga PDP da jam’iyyar Labour Party da kuma APC.
“Daga binciken da aka yi, ya nuna cewa PDP da Labour Party, waɗanda su ne manyan jam’iyyun adawa, na iya fuskantar matsalar ci gaba da wanzuwa a yadda suke a yanzu.
“Abin da binciken ya nuna shi ne cewa jam’iyyun biyu ba za su kasance cikin wani ƙarfi da zai ba su damar tsayar da ‘yan takarar shugaban ƙasa masu ƙarfi a zaɓen gama-gari na 2027 ba,” inji shi.
Tambuwal ya yi zargin cewa ana ƙoƙarin raunana PDP da Labour Party zuwa matsayin ƙananan jam’iyyu, waɗanda a cewar sa galibi kan shiga yarjejeniya da Gwamnatin Tarayya a lokacin zaɓe.
“Wannan shi ne abin da ake son a cimma, kuma ɗaya daga cikin sharuɗɗan shi ne kada Peter Obi ya ci gaba da kasancewa a jam’iyyar Labour domin tsayawa takara,” inji shi.
A cewar sa, wannan lamari ne ya sa ‘yan siyasa masu irin wannan ra’ayi suka yanke shawarar haɗe kai da jam’iyyar ADC domin gina wani dandali mai ƙarfi na adawa.
“Mu ba sababbin shiga ba ne a wannan harkar siyasa. Mun ga alamun tun da wuri, kuma muka yanke shawarar ɗaukar mataki domin daƙile wannan yunƙuri da aka shirya,” inji shi.
Tambuwal ya ƙara da cewa yunƙurin ADC ba wai domin burin mutum ɗaya ba ne, sai dai domin gina wata jam’iyya da za ta mayar da hankali kan jama’a.
“ADC ta shafi jama’a ne kuma ta shafi Nijeriya. A yau, ƙasar nan ta kasu gida biyu: waɗanda ke cikin gwamnati da kuma waɗanda ba su cikin ta.
“Yawancin ‘yan Nijeriya ba su gamsu da halin da ake ciki ba, ciki har da matsalar tsaro, talauci, cin hanci da rashawa da kuma cin amanar amanar jama’a,” inji shi.
Ya jaddada cewa a ƙarshe jama’a ne ke yanke hukunci a zaɓe a Nijeriya, yana mai cewa shugabannin ƙasa da gwamnonin jihohi ma sun taɓa shan kaye a zaɓe idan masu kaɗa ƙuri’a ba su gamsu da jagorancin su ba.
Tambuwal ya nanata cewa sauya sheƙar sa ba domin wata buƙata ta siyasa ta kan sa ba ce, sai dai domin makomar al’ummar sa da kuma makomar Nijeriya baki ɗaya.







