Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana ceto ragowar yara da ma’aikata 130 na Makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke Papiri, Jihar Neja, da aka yi a matsayin “ganin ƙarshen shekara abin so.”
A cikin sanarwar manema labarai da ya fitar a wannan Lahadin, ministan ya tabbatar da cewa dukkan ɗaliban makarantar waɗanda aka sace, su 230, an kuɓutar da su.
“Babu ɗalibi ko guda da ya rage a hannun masu garkuwa,” inji shi.
Idris ya ce an miƙa ɗaliban su 130 ga gwamnatin Jihar Neja, daga nan kuma za a haɗa su da iyalan su.
Ya ƙara da cewa: “Wannan jajircewar da jami’an tsaron mu suka nuna tana sake tabbatar da ƙudirin ƙasar mu na kare al’ummar ta.
“Gwamnatin Tarayya tana miƙa jaje ga iyaye da masu kula da ɗaliban bisa raɗaɗin da satar ta jefa su ciki, tana masu fatan alheri yayin da suke sake haɗuwa da iyalan su, samun cikakkiyar warkewa, tare miƙa gaisuwar wannan lokaci na biki, da kuma Barka da Kirsimeti.”







