Rundunar Haɗin Gwiwa (JTF) tare da goyon bayan sashen sama na Operation Fansan Yamma sun hallaka aƙalla ‘yan bindiga 23 da suke ƙoƙarin tserewa daga Jihar Kano bayan sun kai hare-hare a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa.
Wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Soja na Birged ta 3 na Rundunar Sojin Nijeriya, Manjo Zubairu Babatunde, ya fitar a Kano a yau Lahadi, ta bayyana cewa ‘yan bindigar sun ƙaddamar da hare-haren ne a daren Alhamis zuwa safiyar Juma’a.
Sanarwar ta ce dakarun ƙasa sun daƙile hare-haren cikin nasara tare da yi wa maharan mummunar asara, kafin su bi sawun waɗanda suka tsere zuwa ƙauyen Karaɗuwa a Ƙaramar Hukumar Matazu ta Jihar Katsina.
A cewar Babatunde, rahotannin leƙen asiri sun nuna cewa ‘yan bindigar sun taru a Ɗanmarke da ke Matazu domin binne wasu daga cikin ‘yan’uwan su da aka kashe a yayin artabun da dakarun soji.
Ya ce: “Ɓangaren sama na Sector 2 Operation Fansan Yamma ya gano ‘yan bindigar tare da bibiyar motsin su har sai da baburan su suka taru bayan sun ƙetare wani busasshen rafi,” inji sanarwar. “Daga nan aka kai farmakin sama cikin ƙwarewa, wanda ya yi sanadin hallaka aƙalla ‘yan ta’adda 23, yayin da ake zargin wasu da dama sun jikkata.”
Sanarwar ta ƙara da cewa aikin, wanda ya samu goyon bayan ayyukan leƙen asiri na sama (ISR), ya kuma haifar da lalata makamai da kayan aiki da dama na ‘yan bindigar.
Kwamandan Birged ta 3 na Rundunar Sojin Nijeriya ya yaba wa sashen sama da dakarun ƙasa bisa jarumtaka da jajircewar su a yayin aikin, yana mai cewa, “Jarumtaka da juriya da suka nuna abin a yaba ne.”
Babatunde ya tabbatar da cewa halin tsaro a Jihar Kano na nan cikin kwanciyar hankali, inda dakaru ke ci gaba da sintiri da sa ido a yankunan da abin ya shafa.
Ya ce ƙwazon aiki da ƙwarin gwiwar dakarun na da matuƙar gamsarwa.
Rundunar Sojin Nijeriya ta gode wa al’umma kan goyon bayan da suke bayarwa a yaƙin da ake yi da ‘yan bindiga da ta’addanci, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanai cikin gaggawa.
Ta jaddada cewa sojoji, tare da sauran hukumomin tsaro, za su ci gaba da ɗaukar dukkan matakan da suka dace domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a da tabbatar da tsaron ƙasa.







