Ministan Kuɗi kuma Ministan Daidaita Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, ya bayyana cewa Mission 300, wani shiri na nahiyar Afrika da ke da nufin faɗaɗa samar da wutar lantarki da bunƙasa tattalin arziki, ginshiƙi ne a dabarun tsara tattalin arzikin Nijeriya.
Ministan ya bayyana hakan ne a wannan makon a Abuja lokacin da ya gana da abokan hulɗa na duniya a fannin makamashi da kuɗi kan wannan shiri.
Tattaunawar ta mayar da hankali kan hanzarta aiwatar da shirin da kuma tara jarin zuba hannun jari domin ƙarfafa ɓangaren wutar lantarki na Nijeriya, tare da amincewa cewa tabbatacciyar wutar lantarki muhimmiya ce ga haɓakar aiki, faɗaɗa masana’antu, haɗa jama’a cikin tsarin dijital, da samar da ayyukan yi.
A wajen taron, Edun ya jaddada fara rungumar yarjejeniyar (Compact) da ƙasar ta yi da wuri, kafa haɗaɗɗen sashen aiwatarwa tsakanin Ma’aikatar Kuɗi da Ma’aikatar Wutar Lantarki, da kuma ƙaruwa a fannin makamashin sabuntawa da ake rabawa kai-tsaye, wanda ke samun goyon baya ta hanyar sababbin hanyoyin samar da kuɗi da haɗin gwiwa da ɓangaren ‘yan kasuwa masu zaman kan su.

Daraktar Gudanarwa ta Ayyuka a Bankin Duniya, Anna Bjerde, ta yaba da cigaban sauye-sauyen da Nijeriya ke yi, tana mai bayyana ƙasar a matsayin wacce za ta iya sauya yanayi a shirin ‘Mission 300’ sakamakon girma da jagorancin ta.
Ta ƙara da cewa shirye-shiryen da ake aiwatarwa yanzu haka suna ƙara yawan masu samun wutar lantarki.
Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya jaddada daidaituwar shirin da manufofin tattalin arzikin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai ambaton cigaban da ake samu a gyaran ɓangaren wutar lantarki, saka mitoci, sake fasalin rarraba lantarki, da haɗa tsarin wutar lantarki a matakin yanki.
Dukkan ɓangarorin sun amince da hanzarta aiwatar da shirin, jawo manyan jarin kuɗi, da tabbatar da cewa ‘Mission 300’ ya haifar da tasirin tattalin arziki da ’yan Nijeriya za su iya aunawa.








