• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Nijeriya tana kan hanyar kaiwa ga ƙarfin arziki mai ɗorewa, inji Tinubu

Wakilin Mu by Wakilin Mu
September 27, 2025
in Labarai
A A
0

 

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce tattalin arzikin ƙasar nan ya soma dawowa daidai sakamakon manufofin sauye-sauyen da gwamnatin sa ta aiwatar.

Ya bayyana haka ne a Ibadan, Jihar Oyo, lokacin bikin naɗa Oba Rashidi Ladoja a matsayin Olubadan na 44 na ƙasar Ibadan.

 

Kakakin Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce Tinubu ya bayyana farin cikin sa da yadda ‘yan Nijeriya suka nuna haƙuri da goyon baya a lokacin aiwatar da manufofin.

 

“Ina farin cikin sanar da ku cewa tattalin arzikin mu ya soma gyaruwa, kuma yanzu akwai haske,” inji Tinubu.

 

Shugaban ya kuma yaba da rawar da sabon Olubadan ya taka a tarihin siyasar Najeriya, musamman yadda ya tsallake ƙoƙarin tsige shi daga kujerar gwamnan Jihar Oyo a baya. Ya bayyana shi a matsayin wata alama ta juriyar shugabanci da sadaukarwa ga jama’a.

 

A wajen bikin, Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya miƙa wa Oba Ladoja sandar iko da takardar shaidar zama Olubadan. Ya ce hakan ya kawo ƙarshen jayayya tsakanin dangin sarautar Ibadan.

 

A jawabin sa, sabon Olubadan ya bayyana nadin nasa a matsayin hukuncin Allah, tare da gode wa shugaban ƙasa da gwamnan jihar bisa girmamawa da goyon baya.

Daga cikin manyan baƙi da suka halarci bikin akwai gwamnonin jihohin Ondo, Ekiti, da Osun, tsofaffin gwamnonin Cross River, Osun, Kano da Ogun, tare da shugabannin gargajiya ciki har da Sultan na Sokoto, Alaafin na Oyo da Soun na Ogbomoso.

Previous Post

Tinubu na so jama’a su ƙara haɗa kai yayin da Nijeriya ke cika shekara 65 da zama ’yantacciya

Next Post

Masu wulaƙanta naira ke ƙara haifar da tsadar buga sababbin kuɗi – CBN

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Masu wulaƙanta naira ke ƙara haifar da tsadar buga sababbin kuɗi – CBN

Masu wulaƙanta naira ke ƙara haifar da tsadar buga sababbin kuɗi - CBN

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!