Nijeriya da Dubai za su karɓi baƙuncin taron Investopia a Legas – Tinubu
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa Nijeriya za ta karɓi baƙuncin taron Investopia tare da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a birnin Legas a watan Fabrairu mai zuwa, domin jawo hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.
Shugaban ya bayyana haka ne a yau a yayin taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na 2026.
Ya ce shirin zai taimaka wajen bunƙasa jarin da zai tallafa wa cigaban tattalin arziki mai ɗorewa.
A gefen taron, Nijeriya da UAE sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tattalin arziki ta CEPA, wadda ke da nufin zurfafa haɗin gwiwa a fannonin kasuwanci, makamashi, gine-gine, sufurin kayayyaki da kasuwancin zamani na intanet.
Shugaban UAE, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, tare da ministocin ƙasashen biyu, sun halarci sanya hannun kan yarjejeniyar da Tinubu ya bayyana a matsayin abin tarihi da dabarar bunƙasa dangantakar ƙasashen biyu.
Tinubu ya bayyana cewa Investopia zai haɗa masu zuba jari, ‘yan kasuwa, masu ƙirƙire-ƙirƙire da masu tsara manufofi domin mayar da ra’ayoyi zuwa jarin da zai amfani al’umma.
Ya ce Nijeriya na da burin tara kusan dala biliyan 30 a duk shekara domin ayyukan sauyin yanayi da masana’antu masu kare muhalli, yana mai jaddada buƙatar sauya tsarin hadahadar kuɗin duniya domin sauƙaƙa wa ƙasashe masu tasowa samun jari ba tare da nauyin bashi ba.
Shugaban ya kuma yi nuni da gyare-gyaren makamashi da tattalin arziki da gwamnatin sa ke aiwatarwa, ciki har da Dokar Lantarki ta 2023 da kuma manufofin kasuwar man fetur, yana cewa hakan ya ƙara amincewar masu zuba jari.
Ya ƙara da cewa fitar da kayayyakin da ba na mai ba ta ƙaru da kashi 21 cikin 100, tare da alƙawarin cewa Nijeriya a shirye take ta yi aiki da abokan hulɗa domin gina cigaba mai ɗorewa, adalci da amfani ga kowa.







