Kwamitin Haɗin Gwiwa na Majalisar Wakilai kan Albarkatun Man Fetur ya gayyaci Matatar Ɗangote da Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur na Cikin Teku (NMDPRA) domin warware saɓanin da ke barazana ga ɓangaren man fetur na Cikin teku.
Shugaban kwamitin, Ikenga Ugochinyere, shi ne ya bayyana haka bayan wani taron gaggawa da aka gudanar a Abuja ranar Litinin, inda ya ce tashin hankalin da ke ƙaruwa na iya lalata daidaiton da aka samu kwanan nan.
Ya ce dole ne kwamitin ya ɗauki mataki cikin gaggawa, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin daidaita samarwa, farashi da tsari a sabon tsarin harkokin man fetur na Nijeriya bayan cire tallafin mai.
Ya ce: “Babban batun shi ne sabon rikicin da ya taso sakamakon damuwa da zarge-zargen da Alhaji Aliko Ɗangote ya gabatar kan NMDPRA.
“Muna kare daidaiton da aka samu da ƙyar; samun mafita mai ɗorewa na buƙatar gano muhimman matsaloli, shi ya sa muka gayyaci Ɗangote da shugabannin NMDPRA.”

Ya ƙara da cewa ƙorafe-ƙorafen da aka karɓa sun shafi bayar da lasisin shigo da mai da kuma ko matatun mai na cikin gida za su iya biyan buƙatar man fetur ta kullum a Nijeriya.
Ugochinyere ya ce za a binciki dukkan batutuwan da suka rage lokacin da masu ruwa da tsaki a harkokin tace mai da kula da tsari suka bayyana a gaban kwamitin.







