Hukumar Kula da Hanyoyi da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) ta samu nasarar hukunta mutane 87 da suka karya dokokin zirga-zirga a birnin Kano, ta hanyar Kotun Tafi-da-Gidan-ka da aka kafa domin rage yawaitar take dokokin hanya a cikin birnin.
Bayanin yana ƙunshe cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Hukumar KAROTA, Yusuf Ibrahim Sharaɗa, ya fitar a ranar Juma’a, a Kano.
Ya ce a cikin kwanaki biyu da suka gabata, kotunan da ke gudanar da zama a wurare daban-daban na cikin birnin sun saurari shari’u tare da yanke hukunci kan masu laifin da aka kama suna karya dokokin zirga-zirga, musamman masu wucewa lokacin da alamar hasken ja ya tsarar da su a mahaɗar da danja ke bada hannu.
Sai kuma waɗanda suka aikata wasu laifuka da suka shafi keta dokokin hanya.
Ɗaya daga cikin kotunan da ta gudanar da zama a kusa da Magwan Junction a kan State Road, ta hukunta mutane 41 ƙarƙashin jagorancin Alƙalin Babbar Kotu, Halima Wali.
Haka kuma wani zama da aka gudanar a kan BUK Road kusa da Ƙofar Famfo Junction, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Hauwa Abba, ta hukunta mutane 46 da suka haɗa da direbobi da masu tuƙin A Daidaita Sahu, saboda irin wannan laifi.
Da yake jawabi kan wannan cigaba, Manajan Darakta na KAROTA, Faisal Mahmud Kabir, ya jaddada ƙudirin hukumar na ci gaba da gudanar da zaman kotunan mai tafiya a sassa daban-daban na birnin Kano, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin rage take dokokin hanya da tabbatar da bin doka a tituna.
Ya bayyana cewa wannan mataki ba don tsoratar da direbobi ko masu tuƙa
A Daidaita Sahu ba ne, sai dai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da tsari, bisa manufofin gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Ya kuma yaba da ƙwazon alƙalai, jami’an tsaro da jami’an KAROTA da ke aiki tare wajen aiwatar da wannan aiki, inda ya bayyana cewa jajircewa da kishin aiki ne suka taimaka wajen samun wannan nasara.







