• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Kasafin kuɗin 2026 zai ƙarfafa nasarorin da shirye-shiryen Tinubu ke samu — Minista

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 5, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Idris Ya Ƙaryata Ji-ta-ji-tar An Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa an tsara kasafin kuɗin 2026 ne domin ƙarfafa nasarorin da tsarin shirye-shiryen Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka fara samarwa, waɗanda tuni suka fara nuna sakamako mai kyau.

Ministan ya bayyana haka ne a wani sharhin sa da aka wallafa a jaridun ƙasar nan ranar Litinin, mai taken “Muhimmin Lokaci A Nijeriya: Hujjar Da Ta Sa Hanyar Da Aka Ɗauka Ita Ce Mai Ɓullewa.”

A sharhin, Idris ya ce: “’Kasafin Kuɗin Ƙarfafa Ƙasa, Sabuwar Juriya da Wadata ta Bai-Ɗaya’ yana da matuƙar muhimmanci.

“Alƙawari ne na ƙara himma kan abin da ke aiki, da ƙarfafa nasarori, tare da tabbatar da cewa cigaban bai-ɗaya da muke magana a kai ya zama abin da ‘yan Nijeriya da dama za su fara ji a rayuwar su ta yau da kullum.”

Ya bayyana cewa watanni 31 da suka gabata sun kasance lokaci na sauye-sauye masu wahala amma masu muhimmanci, inda aka ɗauki muhimman matakan tattalin arziki domin kawo ƙarshen durƙushewar da ta daɗe tana addabar ƙasa da kuma gina makoma mai ɗorewa.

Ministan ya ce alamun cigaba sun fara bayyana, inda harkokin kasuwanci suke bunƙasa, amincewar masu zuba jari take ƙaruwa, hauhawar farashi yake raguwa, tare da ƙaruwar ajiyar kuɗaɗen waje.

“Waɗannan ba alƙaluma kawai ba ne. Su ne tubalan ingantaccen sauyi mai ɗorewa a rayuwar yau da kullum ta ‘yan Nijeriya,” inji shi.

Ya kuma jaddada muhimmancin amana da kyakkyawar sadarwa tsakanin gwamnati da al’umma, tare da sake tabbatar da ƙudirin sa na sanar da ‘yan Nijeriya dukkan manufofin gwamnati, ƙalubale da kuma cigaban da ake samu.

Dangane da shirye-shiryen da ke da tasiri kai-tsaye ga rayuwar jama’a, ministan ya bayyana shirin rancen ɗalibai na NELFUND, shirin Shugaban Ƙasa na iskar gas ta CNG domin rage kuɗin sufuri, da shirye-shiryen matasa kamar LEEP, Jubilee Fellows Programme da shirin 3MTT.

Ya kuma ce ana ci gaba da ƙoƙarin magance ƙarancin abinci ta hanyar sake zuba jari a Bankin Manoma da samar da injinan zamani.

A ɓangaren ababen more rayuwa, Idris ya ambaci manyan ayyuka kamar Ginin Babbar Hanyar Gaɓar Teku, Hanyar Sokoto zuwa Badagiri, bututun iskar gas ta AKK, da sabbin ayyukan jirgin ƙasa da ake sa ran za su rage farashi da kuma ƙarfafa haɗin kai a faɗin ƙasa.

Game da tsaro, ministan ya ce gwamnati na ƙara ɗaukar jami’ai, inganta kayan aiki, da kuma ƙarfafa haɗin gwiwar ƙasashen waje.

Ya kawo misalin ceto ɗaliban da aka sace kwanan baya a jihohin Kebbi da Neja a matsayin shaida ta sabon ƙudiri da mayar da hankali kan batun tsaro.

Duk da haka, ya amince cewa ‘yan Nijeriya da dama suna fama da wahalhalu, amma ya tabbatar da cewa gwamnati na ƙoƙarin hanzarta kawo sauƙi ta hanyar ci gaba da aiwatar da gyare-gyare.

Ya yi kira ga jama’a da su ɗauki gina ƙasa a matsayin wani nauyi da ya rataya a wuyan kowa, su shiga cikin tattaunawa mai amfani, su kare kadarorin jama’a, tare da ƙin yarda da yaɗa labaran ƙarya.

Ministan ya yaba wa Shugaban Kasa Tinubu bisa jagoranci mai natsuwa da jajircewar sa, inda ya ce hulɗar da aka yi kwanan nan da Amurka ta taimaka wajen ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu da kuma yaƙi da ta’addanci.

Yayin da sabuwar shekara take kankama, Idris ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su ci gaba da mai da hankali kan gaba.

“Mun shimfiɗa sabon tubali. Yanzu kuma dole mu gina gidan tare,” inji shi.

A ƙarshe, Idris ya sake jaddada cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai za ta ci gaba da kasancewa ƙofar ta a buɗe take, mai aiki tuƙuru tare da daidaito wajen bayyana manufofi da ayyukan gwamnati, tare da yi wa dukkan ‘yan Nijeriya fatan zaman lafiya da shekara mai albarka.

Previous Post

Sarkin Kano Sanusi ya jinjina wa CBN, ya ce Nijeriya ta tsallake siraɗin rugujewar rattalin arziki

Next Post

Ba da yawu na Sa’idu Enagi ya yi rubutu kan siyasar Neja ba, kuma na dakatar da shi – Ministan Yaɗa Labarai

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Next Post
Ba da yawu na Sa’idu Enagi ya yi rubutu kan siyasar Neja ba, kuma na dakatar da shi – Ministan Yaɗa Labarai

Ba da yawu na Sa'idu Enagi ya yi rubutu kan siyasar Neja ba, kuma na dakatar da shi - Ministan Yaɗa Labarai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!