• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

‘Harajin Hajji’: Gwamnatin Tarayya za ta iya samun ₦5.4bn daga alhazai a bana

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 10, 2026
in Labarai
A A
0
Gwamnatin Tinubu ta rage kuɗin zuwa aikin Hajji
Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman

Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman

An yi hasashen cewa Gwamnatin Tarayya za ta tara kimanin ₦5.4 biliyan daga alhazan Nijeriya da za su halarci aikin Hajjin 2026, ta hanyar wasu kuɗin hidima na dole da aka sara wa mahajjata.

Wata ƙungiya mai zaman kan ta mai suna Independent Hajj Reporters (IHR) ita ce ta yi wani nazari da ta fitar kwanan nan a cikin sanarwar manema labarai, to inda ta ce tsarin kuɗin Hajjin 2026 ya wajabta wa kowane alhaji ya biya kashi 2 cikin ɗari a matsayin kuɗin hidima kai-tsaye zuwa Babban Bankin Nijeriya (CBN).

Da yake farashin Hajji a hukumance ya kai kusan ₦7.6 miliyan ga kowane mutum, wannan harajin na dole ya kai kimanin ₦136,417 ga kowane alhaji.

Idan aka yi la’akari da rarraba mahajjata 40,000 ga jihohi daban-daban, an ƙiyasta cewa jimillar kuɗin da zai shiga asusun CBN zai kai tsakanin ₦5.3 biliyan zuwa ₦5.4 biliyan. A dalar Amurka, kuɗin ya kai $92.46 ga kowane mutum, wato jimillar kusan $3.7 miliyan.

Wannan adadi ya ƙaru idan aka kwatanta shi da $90 da aka caja a lokacin Hajjin 2025.

Ƙungiyar, wadda ke sa ido kan gaskiya da bayyana gaskiya a harkokin Hajji, ta bayyana cewa an fi amfani da wannan kuɗi ne wajen canja wurin kuɗaɗe zuwa asusun bankin ƙasashen waje na Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) da ke Saudiyya.

Tun a watan Oktoba 2025, ƙungiyar ta IHR ta roƙi gwamnati da ta soke wannan caji, tana bayyana shi a matsayin “nauyin kuɗi da ba dole ba” da aka ɗora wa ‘yan ƙasa da tuni suke fuskantar tsadar kuɗaɗe daga hukumomin gwamnati daban-daban.

“Karɓar wannan manyan kuɗi na nuna cewa aikin Hajji ya zama wata babbar hanyar samun kuɗaɗen shiga ga gwamnati, fiye da ɓangarorin sa na addini da gudanarwa,” inji ƙungiyar.

Duk da tattaunawar da ake ci gaba da yi, CBN ko kuma gwamnatin Tinubu ba su sanar da yin duba ko soke wannan tsari ba.

Majiyoyi da ke da kusanci da lamarin sun nuna cewa har yanzu tsarin yana nan daram.

IHR ta yi kira ga gwamnati da CBN da su bayyana hujjar wannan caji a fili, tare da samar da cikakken bayani kan yadda ake amfani da kuɗaɗen.

Haka kuma, ta buƙaci Majalisar Tarayya da ta binciki yadda kuɗin ke gudana, domin tabbatar da cewa ba a ɗora wa mahajjata nauyin kuɗi fiye da ƙima ba, musamman waɗanda ba su da bayyanannen amfani ga tafiyar su ta ibada.

Tags: HajjiharajiIHRNAHCON
Previous Post

Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025

Next Post

Tinubu ya sauka Abu Dhabi don halartar taron ADSW 2026

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Tinubu ya sauka Abu Dhabi don halartar taron ADSW 2026

Tinubu ya sauka Abu Dhabi don halartar taron ADSW 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!