An yi hasashen cewa Gwamnatin Tarayya za ta tara kimanin ₦5.4 biliyan daga alhazan Nijeriya da za su halarci aikin Hajjin 2026, ta hanyar wasu kuɗin hidima na dole da aka sara wa mahajjata.
Wata ƙungiya mai zaman kan ta mai suna Independent Hajj Reporters (IHR) ita ce ta yi wani nazari da ta fitar kwanan nan a cikin sanarwar manema labarai, to inda ta ce tsarin kuɗin Hajjin 2026 ya wajabta wa kowane alhaji ya biya kashi 2 cikin ɗari a matsayin kuɗin hidima kai-tsaye zuwa Babban Bankin Nijeriya (CBN).
Da yake farashin Hajji a hukumance ya kai kusan ₦7.6 miliyan ga kowane mutum, wannan harajin na dole ya kai kimanin ₦136,417 ga kowane alhaji.
Idan aka yi la’akari da rarraba mahajjata 40,000 ga jihohi daban-daban, an ƙiyasta cewa jimillar kuɗin da zai shiga asusun CBN zai kai tsakanin ₦5.3 biliyan zuwa ₦5.4 biliyan. A dalar Amurka, kuɗin ya kai $92.46 ga kowane mutum, wato jimillar kusan $3.7 miliyan.
Wannan adadi ya ƙaru idan aka kwatanta shi da $90 da aka caja a lokacin Hajjin 2025.
Ƙungiyar, wadda ke sa ido kan gaskiya da bayyana gaskiya a harkokin Hajji, ta bayyana cewa an fi amfani da wannan kuɗi ne wajen canja wurin kuɗaɗe zuwa asusun bankin ƙasashen waje na Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) da ke Saudiyya.
Tun a watan Oktoba 2025, ƙungiyar ta IHR ta roƙi gwamnati da ta soke wannan caji, tana bayyana shi a matsayin “nauyin kuɗi da ba dole ba” da aka ɗora wa ‘yan ƙasa da tuni suke fuskantar tsadar kuɗaɗe daga hukumomin gwamnati daban-daban.
“Karɓar wannan manyan kuɗi na nuna cewa aikin Hajji ya zama wata babbar hanyar samun kuɗaɗen shiga ga gwamnati, fiye da ɓangarorin sa na addini da gudanarwa,” inji ƙungiyar.
Duk da tattaunawar da ake ci gaba da yi, CBN ko kuma gwamnatin Tinubu ba su sanar da yin duba ko soke wannan tsari ba.
Majiyoyi da ke da kusanci da lamarin sun nuna cewa har yanzu tsarin yana nan daram.
IHR ta yi kira ga gwamnati da CBN da su bayyana hujjar wannan caji a fili, tare da samar da cikakken bayani kan yadda ake amfani da kuɗaɗen.
Haka kuma, ta buƙaci Majalisar Tarayya da ta binciki yadda kuɗin ke gudana, domin tabbatar da cewa ba a ɗora wa mahajjata nauyin kuɗi fiye da ƙima ba, musamman waɗanda ba su da bayyanannen amfani ga tafiyar su ta ibada.







