• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Ilimi

Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai

Wakilin Mu by Wakilin Mu
October 23, 2025
in Ilimi
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani shiri na horas da matasa fiye da 260,000 a fannonin sana’o’in dogaro da kai a faɗin ƙasar nan, ƙarƙashin shirin Technical and Vocational Education and Training (TVET).

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, shi ne ya bayyana hakan a yau Alhamis yayin da yake duba wasu cibiyoyin gudanar da shirin a birnin Abuja.

A cewar sa, gwamnati na da burin horas da sama da matasa 900,000 a matakai daban-daban na wannan shiri domin ba su damar samun ƙwarewa da za ta ba su ikon dogaro da kan su tare da inganta tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce: “Muna da cibiyoyi sama da 2,600 a fadin kasar nan. Wannan mataki na farko zai kunshi mutum 260,000, kuma mataki na gaba zai ƙara kusantar da mu burin horas da mutum 960,000.”

Alausa ya ƙara da cewa shirin yana gudana a dukkan jihohin ƙasar nan da kuma Gundumar Babban Birnin Tarayya.

Ya kuma tabbatar wa da mahalarta cewa za su samu kuɗin tallafi da kayan farawa bayan kammala horo, domin su kafa ƙananan sana’o’in su.

Ministan ya bayyana shirin a matsayin wani ɓangare na hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen farfaɗo da ilimin sana’a da kuma ƙarfafa tsarin TVET a matsayin ginshiƙin ilimin ƙasar nan.

Ya ce Shugaban Ƙasa ya amince da ware kashi 5% na kasafin TETFund domin tallafa wa cigaban shirin TVET a duk shekara, abin da ya bayyana a matsayin matakin ɗorewar shirin.

An kaddamar da shirin TVET tun a watan Yuni, a matsayin wani ɓangare na yunƙurin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa ilimin sana’o’i da haɓaka damar aikin yi ga matasa.

Shirin, wanda zai ɗauki lokaci tsakanin watanni shida zuwa goma sha biyu bisa ga irin sana’ar, ya ƙunshi fannonin kiwon dabbobi, kiwon kifi, ƙera tukwane na zamani, da sauran sana’o’in hannu.

A halin yanzu, ana gudanar da horon ne a cikin cibiyoyi sama da 2,600 a faɗin Nijeriya.

Tags: horaswailimimatasaTunji Alausa
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Jihar Neja Bisa Fashewar Tankar Mai a Essa

Next Post

Tinubu ya sauya Hafsan Hafsoshin Tsaro, ya naɗa Janar Oluyede a muƙamin 

Related Posts

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya
Ilimi

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

April 26, 2026
NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795
Ilimi

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795

April 19, 2026
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi
Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

March 15, 2026
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ilimi

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

February 18, 2026
Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista
Ilimi

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

January 24, 2026
Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano
Ilimi

Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano

January 20, 2026
Next Post
Tinubu ya sauya Hafsan Hafsoshin Tsaro, ya naɗa Janar Oluyede a muƙamin 

Tinubu ya sauya Hafsan Hafsoshin Tsaro, ya naɗa Janar Oluyede a muƙamin 

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!