Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya kai ziyarar ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kano da jama’ar jihar kan kisan gillar da aka yi wa maharba ‘yan asalin jihar su 16 a Uromi.
Da yake jawabi a Gidan Gwamnatin jihar, Okpebholo ya bayyana kisan da abin baƙin ciki kuma ya ba da tabbacin cewa an kama mutum 14 da ake zargi da aikata wannan ta’asar.
Ya ba da tabbacin cewa za a hukunta su, sannan su kuma iyalan mamatan za a biya su diyya.
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga Gwamna Okpebholo da ya tabbatar da cewa an gurfanar da waɗanda suka tafka wannan mugun abu a gaban ƙuliya.
Gwamna Yusuf ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta fito ta bayyana sunayen waɗanda aka kama kuma ta tabbatar da cewa an biya diyya ga iyalan waɗanda aka halaka.







