Kwanan nan an riƙa watsa wasu bayanan shaci-faɗi waɗanda suka haddasa aka riƙa yin ɓaɓatu cewa wai Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta yi wa Jihar Legas kasafin ayyukan raya ƙasa, har na Naira tiriliyan 3.9 ita kaɗai. Idan mutum ya kalli alƙaluman bayanan zai ga cewa gwamnati ta fifita: kai ka ce an maida asusun gwamnatin tarayya zuwa asusun raya Legas.
Amma idan idan mutum ya bi bayanan waɗanda aka watsa a tsanake, zai fahimci cewa da gangan ne wasu suka dunƙule ayyukan raya ƙasa daban-daban, waɗanda suka haɗa da manyan titunan gwamnatin tarayya, ayyukan titin Bakin Teku da sauran ayyukan wasu titunan, duk suka kira su “manyan ayyukan raya Legas.”
To idan haka ne, kenan sai a kira aikin titin Kano zuwa Maiduguri cewa “ayyukan Maiduguri ne ita Kaɗai.” Ashe kenan wannan shaci-faɗi bai bi diddigin gaskiyar yadda gwamnati ke gudanar da ayyukan raya ƙasa ba.
Domin idan aka yi wa bayanan ayyukan raya ƙasa waɗanda gwamnatin Tinubu ta yi da waɗanda take kan yi filla-filla, za a gane cewa ayyukan da Legas ta ci moriya na ita kaɗai baki ɗaya na Naira tiriliyan 1.2 ne. Wannan fa idan aka haɗa da aikin filin jirgi, gyaran Gadar Carter da sauran gyare-gyare nan da can a cikin Legas ɗin.
Sauran ayyukan Naira tiriliyan 2.7 kuma na manyan tituna ne waɗanda suka bi Jihar Legas suka zarce suka nufi sauran sassan jihohin ƙasar nan. Saboda haka a daina cewa Legas ta yi wa kasafin Najeriya haɗiyar-lomar-tuwo. Abin da ke faruwa shi ne mafi alfanu: Ayyukan da wannan gwamnati ke yi yana karaɗe dukkan birane, yankuna zuwa yankuna da tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya.
Ayyukan Gwamnatin Tinubu A Arewa Maso Yamma
. Arewa Maso Yamma: Naira Tiriliyan 5.97 (fiye da kashi 40% na dukkan ayyukan da aka sa wa hannun amincewa).
. Kudu Maso Kudu: Naira tiriliyan 2.41.
. Arewa Ta Tsakiya: Naira tiriliyan 1.13.
. Kudu Maso Gabas: Naira Biliyan 407
. Arewa Maso Gabas: Naira Biliyan 400.
. Kudu Maso Yamma (banda Legas): Naira Biliyan 604.
. Ayyukan Legas Kacokan: Naira Tiriliyan 1.2.
Saboda haka dalla-dalla da filla-fillar waɗannan alƙaluman bayanai sun tabbatar da cewa yankin Arewa Maso Yamma ne ya fi samun amincewar yi masu ayyukan raya ƙasa daga gwamnatin tarayya masu ɗimbin yawa, ba Legas ba.
Ayyukan Raya Ƙasa Na Al’ummar Ƙasa Ne Ba Garabasar Wata Mazaɓa Ba Ce:
To a nan ya zama tilas a maida hankali kan wannan cacar-baki da mahawara dangane da ayyukan raya ƙasa. A daina kallon irin waɗannan ayyuka a matsayin wata shiyya ko yanki ɗaya ne kaɗai zai ci moriyar sa. Tituna, gadoji titin jirgin ƙasa da ayyukan wutar lantarki duk na kowa ne, ba na ɓangare ɗaya ba. Ba a ware wani ɓangare an ce su kaɗai za su yi amfani da su ba. Ayyuka ne tamkar jijiyoyin da suka haɗe wuri ɗaya ta hanyar ci gaba da raya tattalin arzikin ƙasa.
Manomin da ke Katsina yana da buƙatar cin kasuwar Legas. Ɗan tireda a garin Aba ya dogara kan safarar kaya daga Aba har Kano. Ɗalibi a Sokoto yana buƙatar wutar lantarki ta ƙasa, kamar yadda ɗalibin da ke garin Fatakwal ke buƙata. Saboda haka a riƙa duba cewa ayyukan raya ƙasa ana yin su ne domin kaiwa ga dukkan sassan ƙasa daga inda aka yi su. Har su isa sassa na duniya.
To kuwa don an taru a wani gari ko wuri an buɗe aikin raya ƙasa, hakan ba yana nufin na su kaɗai ba ne.
Abubuwan da irin waɗannan ayyukan raya ƙasa ke amfana sun haɗa da hada-hadar cinikayya da kasuwanci, inganta makamashi, sai kuma damammakin da ke bijirowa ga al’umma na gada wurare daban-daban, idan aka samar da waɗannan tituna da cibiyoyin hasken lantarki.
Yadda Alƙiblar Gwamnatin Tinubu Ke Fuskantar Arewa Maso Yamma:
Bari mu yi bayani ƙarara: ba don ƙuri’un Arewa Maso Yamma ba, to da Tinubu bai kai labari a takarar zaɓe ba. Kuma shi Shugaban Ƙasa ya san haka. Bai manta ba, bai kuma kasance maras godiya ba. Ashe kenan, bai ci moriyar ganga ya yada kwauren ta ba.
A dubi aikin Tashar Samar da Lantarki ta Kaduna, wadda za ta samar da miga wat 255, wanda aka bijiro da shi zamanin gwamnatin marigayi Umaru Musa Yar’adua, amma aka watsar da shi tsawon shekaru. A yau ana ta ƙoƙarin farfaɗo da aikin a ƙarƙashin Tinubu.
Wannan tasha ba kawai samar da lantarki za ta yi ba; ta zama abin alfahari da ɗorewar alƙawarin Arewa baki ɗaya.
Ga kuma titin Kaduna zuwa Kano, ga titin Kano zuwa Maiduguri. Ga aikin titin Sokoto zuwa Illela, sai kuma gagarimin aikin bunƙasa fannin ilimi da inganta tsaro. Waɗannan ba fa ƙananan ayyuka ba ne. An bijiro da su ne domin nuna wa Arewa Maso Yamma cewa su ne a sahun farko na samar wa ayyukan bunƙasa ƙasa, a tsare-tsaren inganta yankin tun tashin farko na ayyukan da wannan gwamnati ta soma. Yanzu ma aka soma. Yayin da aka kammala tsarawa da amincewa da Aikin Titin Karaɗe Ƙasa wanda zai haɗa Kalaba har zuwa Maiduguri, na daga Sokoto a Arewa Maso Yamma, to za a ga gagarimin ci gaban sabon tsarin ayyukan raya ƙasa.
Wannan ƙasaitaccen aiki guda ɗaya tilo zai haɗe yankunan Kudu Maso Kudu, Arewa Ta Tsakiya, Arewa Maso Gabas da Arewa Maso Yamma, ta hanyar samar da titunan da za su tashi daga wannan yanki su dangana wancan yanki, da nufin samar da dogon kadarkon sufuri da zirga-zirgar bunƙasa tattalin arziki, samar da ayyuka. Baya ga ciyar da waɗannan yankuna gaba, za kuma ya kasance wani gwadaben sufuri tsakanin Najeriya da ƙasashen Afirka.
Babbar ribar ayyukan dai ita ce tattalin arzikin mu ne zai amfana, haka manoman ƙasar nan masu ƙwazo, jajirtattun ‘yan tiredar mu, masu masana’antu da masu motocin sufuri da zirga-zirga duk za su ci moriyar wannan aiki.
Idan ana gudanar da zirga-zirga a ƙanƙanin lokaci, za a rage tsadar safarar kayayyaki daga gari zuwa gari kenan. Za a samu bunƙasar kasuwanni da kasuwanci, arziki zai ƙara yalwa a faɗin ƙasa, sannan za a samu ƙari da faɗaɗar albarka a ƙasa baki ɗaya.
Sharrin ‘Yan Farfaganda Kan Gwamnatin Tinubu:
Hatsarin da ke tattare da jadawalin kuɗaɗen ayyukan da wasu ‘yan bankaura suka ƙirƙiro, suka watsa, ba fa kuskure ne kaɗai ba. Da gangan suka yi haka, domin su haddasa ƙiyayya a zukatan jama’a: Sun yi domin su Legas da Kano gaba, su cusa ƙiyayya tsakanin Kudu Maso Yamma da Arewa Maso Yamma, tsakanin wannan yanki da wancan kuma an fifita ɗaya, an maida ɗaya saniyar-ware. Wannan kuma gillin siyasa ne.
Amma su ‘yan Najeriya wayayyu ne:
. Legas na nan a matsayin ta na cibiyar hada-hadar kasuwanci da cinikayyar Najeriya. Ta cancanci gyare-gyaren da ake yi mata.
. Arewa Maso Yamma nan ne ruhin siyasar Najeriya, kuma bangon jingina domin samun nasarar lashe zaɓe. Daidai ne da ake wa manyan ayyukan da aka yi, kuma ake kan yi.
. Kowane yanki ko shiyya ya samu haƙƙin ayyukan da suka wajaba ya samu, saboda kasafin kuɗaɗen gwamnatin Tinubu na tattalin arzikin bai-ɗaya ne, na ƙasa ɗaya ce, na al’umma ɗaya ce.
Gwamnatin Tinubu: Ƙwalelen Ku Masu Yaɗa Ji-ta-ji-ta:
Tarihi dai ba zai tuna wannan shirme na jadawalin adadin kuɗaɗen ƙarya da ku ka ce gwamnatin Tinubu ta kashe wa Legas ita kaɗai ba. Sai dai tarihi zai riƙa tuna wa manoma a Katsina waɗanda a yanzu kayan su ke isa sabbin kasuwanni, zai tuna aikin samar da lantarki a Kaduna, wanda ‘Yar’Adua ya bijiro da shi, amma Tinubu ya farfaɗo da shi. Sai kuma makarantu da asibitocin da ake ginawa a Sokoto da Zamfara.
Shugaba Tinubu bai juya wa Arewa baya ba. Ya yi amanna da yankin, kuma yana kan samar da manyan ayyukan inganta rayuwa a yankin.
Wannan kuwa a bayyane komai yake. Kuma gaskiyar magana kenan.
Saboda haka wani zanen bogi na jadawalin ƙarairayin fifita Legas kan Arewa Maso Yamma da ‘yan ƙarambosuwa ke yaɗawa, yaudara ce kawai, ba za su iya shafe ayyukan da Tinubu ya samar ba.
* Yakubu Shi Na Babban Darakta, Ofishin Kasafin Kuɗaɗe Na Tarayya







