• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Me ya sa har yanzu ake ciwo bashi bayan Tinubu ya cire tallafin mai? – Sarki Sanusi

ALI KANO by ALI KANO
April 24, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Me ya sa har yanzu ake ciwo bashi bayan Tinubu ya cire tallafin mai? – Sarki Sanusi
Mai Martaba Sarkin Kano, Dakta Muhammadu Sanusi II

Mai Martaba Sarkin Kano, Dakta Muhammadu Sanusi II

Mai Martaba Sarkin Kano, Dakta Muhammadu Sanusi II, ya nuna damuwa kan yadda Gwamnatin Tarayya take ci gaba da dogaro da karɓar bashi duk da cire tallafin man fetur da ta yi, inda ya yi tambaya kan alƙiblar da harkokin kuɗin ƙasar nan suke fuskanta da ɗorewar su.

Sanusi, wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne, ya bayyana hakan ne a wata hira da aka watsa a gidan talbijin na News Central TV a yau Juma’a, inda ya yi nazari mai zurfi kan halin da harkokin kuɗin Nijeriya suke ciki a yanzu.

Duk da yake ya amince cewa cire tallafin mai da sassauta tsarin canjin kuɗaɗen waje gyare-gyare ne da suka zama dole, ya yi gargaɗin cewa rashin dacewar lokacin aiwatar da su da kuma rashin tsauraran matakan kula da harkokin kuɗi na iya lalata fa’idojin da ake tsammani.

A cewar sa, dogon tarihin da Nijeriya ke da shi na tallafa wa matatun mai na ƙasashen waje tare da yin watsi da ƙarfin tace mai na cikin gida yana nuna wata matsala ce ta tsarin da ya kamata a gyara.

Sarkin ya ce: “Tun da daɗewa nake cewa tsarin tallafin mai ba mai ɗorewa ba ne. Ba za mu ci gaba da tallafa wa matatun mai na ƙasashen waje ba. Mu ƙasa ce mai samar da mai. Ba zai yiwu mu riƙa raya matatun waje alhali namu ba sa aiki ba.”

Sai dai ya nuna kyakkyawan fata kan sababbin cigaban da aka samu a fannin, yana mai cewa an fara karkata zuwa tace mai a cikin gida tare da rage dogaro da shigo da man fetur daga waje.

Ya ce: “A yau muna da yanayin da muke da matatar mai tamu a cikin gida. Ba ma shigo da kayan man fetur. Har ma muna fitarwa zuwa Turai, kuma wannan abu ne mai kyau ga tattalin arziki.”

Duk da goyon bayan da yake bai wa gyare-gyaren, Sanusi ya nuna damuwa kan yadda aka tsara su da kuma lokacin da aka aiwatar da su, yana mai cewa akwai wasu muhimman matakai da wataƙila an yi watsi da su.

“Tsarin canjin kuɗi na bogi, musamman idan ana buga kuɗi, ba zai yi aiki ba. Dole ne a samu faɗuwar darajar kuɗi,” inji shi.

“Ni a gani na, cire tallafi ko sassauta canjin kuɗi abubuwa ne masu kyau. Amma shin an yi su a daidai lokacin da ya dace? Wannan tambaya ce. Shin akwai wasu abubuwan da ya kamata a yi amma ba a yi su ba? Waɗannan ma wasu batutuwa ne.”

Ya ce aiwatar da sassauta canjin kuɗi a yanayin da tsarin kuɗi yake da sassauci ya taimaka wajen faɗuwar darajar naira sosai.

“Ba ya isa a ce an cire tallafi kawai. Dole ne a cire shi. Idan ka kai matsayin da kaso 100 na kuɗaɗen shiga naka ke tafiya wajen biyan bashin da aka ci, ba za ka iya ci gaba a haka ba. To daga ina kuɗin za su fito?

“Amma idan ka cire tallafi kuma ka sassauta canjin kuɗi a yanayin da babu tsauraran matakan kula da yawan kuɗi, kafin ka daidaita yawan kuɗin da ke yawo, naira za ta faɗi ƙasa warwas. Wannan matsalar lokaci ce.”

Sanusi ya kuma tambayi dalilin da ya sa gwamnati take ci gaba da karɓar bashi mai yawa bayan cire biyan tallafi.

Ya ƙara da cewa: “Mun cire tallafi. Yanzu muna amfani da kuɗin. Abin da bai kamata mu gani ba shi ne rashin daidaita harkokin kuɗi. Ba za ka rage almubazzaranci sannan ka ci gaba da karɓar bashi ba. Na faɗi haka tun da farko. Ya kamata a ga amfanin hakan.

“Idan ba ka biyan tallafi kuma kana da kuɗin, me ya sa har yanzu muke ci gaba da karɓar bashi? Don me ake karɓar bashin?”

Sababbin alƙaluma sun ƙara tabbatar da damuwar sa. Rahotanni a watan Afrilu sun nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta ƙara shirin karɓar bashin shekarar 2026 da tiriliyan ₦11.31, wanda ya kai jimillar bashin da ake sa ran za a karɓa zuwa tiriliyan ₦29.20.

A wani labarin mai alaƙa da wannan, yanzu haka Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nemi amincewar Majalisar Dattawa kan sabon bashin dala miliyan 516 da yake nema domin tallafa wa aikin babbar hanyar Sakkwato zuwa Badagiri.

Tags: bashiMuhammaduSanusiIISarkin Kano
Previous Post

Sabon tsarin leƙen asiri da bayanan sirri sun fara haifar da ɗa mai ido – Idris

Next Post

Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin Ministan Gidaje

Related Posts

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa

May 3, 2026
Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda

May 1, 2026
Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

May 1, 2026
Cikar wa’adin ƙarfafa jari: Yadda bankunan Nijeriya suka bazama tara Naira tiriliyan 4.6 a ƙoƙarin cika sharuɗɗan CBN
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Juyin Zamani: Yadda CBN ke ƙarfafa wa ɗalibai koyon ilmin sarrafa kuɗi, yayin da tattalin arziki ke sauyawa a zamanance 

April 30, 2026
Yadda asusun kuɗaɗen waje na Nijeriya zai cika maƙil, bayan CBN ya yi wa naira allurar ƙarin ƙarfin wujijjiga dala a tsakiyar kasuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda CBN ke ta ƙoƙarin daƙile malejin hauhawar farashi zuwa ƙasa da kashi 10 bisa 100

April 29, 2026
Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

April 27, 2026
Next Post
Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin Ministan Gidaje

Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin Ministan Gidaje

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!