• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Shugaban Ƙasa ya taya Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris Malagi murnar cika shekaru 60

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
May 1, 2026
in Labarai
A A
0
Shugaban Ƙasa ya taya Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris Malagi murnar cika shekaru 60
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana musabaha da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana musabaha da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da saƙon taya murna ga Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris Malagi, murnar cikar sa shekaru 60 da haihuwa, wanda ya kama ranar 2 ga Mayu, 2026.

A saƙon, wanda ya rattaba wa hannu da kan sa, Shugaban Ƙasa ya ce: “Mohammed ƙwararren mai sadarwa ne, ƙwararren masani a harkar hulɗa da jama’a, kuma jagora a fannin kafafen yaɗa labarai wanda ya kawo ƙwarewa, amana da ɗaukar nauyi a harkar sadarwar gwamnati a cikin wannan mulki namu.

“Sunan sa ya riga ya yi masa shaida. Ya kasance a sahun gaba a masana’antar yaɗa labarai da hulɗa da jama’a a matsayin wanda ya kafa kuma mai wallafa jaridar Blueprint, haka kuma shugaban wani kamfanin hulɗa da jama’a da ya cimma nasara, sannan gidan rediyo.

“Matsayin da ya riƙe na Babban Sakataren Ƙungiyar Masu Mallakar Jaridu ta Nijeriya (NPAN) kafin naɗin sa ya nuna shi a matsayin mai kishin ƙasa kuma abokin aiki mai muhimmanci wajen gina ƙasa.

“Ina yaba wa Mohammed bisa ƙwazo, basira da jajircewar sa wajen isar da nasarori, manufofi da shirye-shiryen wannan gwamnati tamu.

“Ya kasance mai tsayawa tsayin daka wajen yaɗa saƙon Sabon Fata a faɗin ƙasar nan, kuma ina ƙarfafa masa gwiwa da ya ci gaba da kyakkyawan aikin da yake yi.

“Yayin da Mohammed yake bikin wannan muhimmiyar ranar haihuwa, ina tare da iyalan sa da abokan sa wajen yi masa fatan ƙarin shekaru masu yawa cikin ƙoshin lafiya da ƙarfi yayin da yake ci gaba da hidimta wa ƙasa.

“Bola Ahmed Tinubu, Shugaban Ƙasa kuma Babban Kwamandan Rundunar Sojojin Nijeriya, Jamhuriyar Tarayyar Nijeriya, 1 ga Mayu, 2026.”

Tags: Mohammed Idrismurnar zagayowar ranar haihuwaShugaba Bola Ahmed Tinubutaya murna
Previous Post

Ƙungiyar al’ummar Birnin-Gwari ta yaba wa Gwamna Uba Sani kan aikin gyaran hanya na ₦178 biliyan da kuma dawo da zaman lafiya

Next Post

Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!