• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Hajjin 2026: Gwamnatin Tarayya na nazarin hanyoyin rage tsadar man jiragen sama, ta kuma ba da tabbacin za a yi jigilar maniyyata ba tare da tangarɗa ba

* Za a fara tashi zuwa aikin Hajjin 2026 a ranar 3 ga Mayu, 2026

Fati Abdul by Fati Abdul
April 30, 2026
in Labarai
A A
0
Hajjin 2026: Gwamnatin Tarayya na nazarin hanyoyin rage tsadar man jiragen sama, ta kuma ba da tabbacin za a yi jigilar maniyyata ba tare da tangarɗa ba
Alhazan Nijeriya suna hawa jirgin sama domin tafiya aikin Hajj

Alhazan Nijeriya suna hawa jirgin sama domin tafiya aikin Hajj

Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Nijeriya, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tana duba hanyoyi daban-daban domin tallafa wa kamfanonin jiragen saman Nijeriya, ciki har da waɗanda ke jigilar alhazai, wajen rage tasirin tashin farashin man jiragen sama a duniya kafin gudanar da aikin Hajjin 2026.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Fatima Sanda Usara, ta fitar a yau Alhamis, an ambato Yusuf yana magana ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen aikin hajjin.

Yusuf ya ce hukumar tana ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki a fannin zirga-zirgar jiragen sama domin tabbatar da ingantacciyar jigilar maniyyata ba tare da wata matsala ba.

Ya ƙara da cewa tattaunawa kan harkokin aiki, musamman batun man jiragen sama, wani ɓangare ne na yau da kullum a shirye-shiryen kafin hajji, kuma ana gudanar da shi ne cikin tsarin da aka saba.

Ya ƙaryata rahotannin da ke cewa wasu daga cikin kamfanonin jiragen saman da aka ɗauka ba sa son shiga aikin jigilar alhazai saboda tsadar mai, inda ya bayyana irin waɗannan rahotanni a matsayin hasashe marar tushe kuma ba sa nuna yadda ake haɗin kai tsakanin gwamnati da masu aiki a halin yanzu.

“Don kauce wa shakku, duk shirye-shiryen da ake buƙata suna tafiya yadda aka tsara, kuma an sa ranar fara jigilar maniyyata ta Hajjin 2026 a ranar 3 ga Mayu, 2026,” inji shi.

Yusuf ya kuma bayyana cewa shigar da Gwamnatin Tarayya cikin lamarin na nufin tabbatar da daidaito, ta yadda kamfanonin jiragen sama ba za su yi asara ba, haka kuma maniyyata ba za su fuskanci tsadar kuɗin tikiti mai yawa ba.

Ya ƙara da cewa duk kamfanonin jiragen saman da aka ɗauka domin aikin hajjin sun sake jaddada kudirin su na tabbatar da tsaro, inganci, da kuma gudanar da aiki ba tare da wata tangarɗa ba, yayin da tattaunawa da hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki ke ci gaba.

Duk da matsin tattalin arziki da ake fuskanta, shugaban hukumar ya nuna ƙwarin gwiwa cewa duka jigilar maniyyata zuwa da dawowa daga Hajjin 2026 za su gudana cikin nasara.

Ya sake jaddada fatan hukumar cewa, tare da ci gaba da tallafin gwamnati da kuma kyakkyawan haɗin kai, maniyyatan Nijeriya za su samu ingantaccen aikin hajji mai nasara a shekarar 2026.

Tags: Ambasada Ismail Abba YusufHajji2026jigilajirage
Previous Post

Yadda CBN ke ta ƙoƙarin daƙile malejin hauhawar farashi zuwa ƙasa da kashi 10 bisa 100

Next Post

Juyin Zamani: Yadda CBN ke ƙarfafa wa ɗalibai koyon ilmin sarrafa kuɗi, yayin da tattalin arziki ke sauyawa a zamanance 

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Cikar wa’adin ƙarfafa jari: Yadda bankunan Nijeriya suka bazama tara Naira tiriliyan 4.6 a ƙoƙarin cika sharuɗɗan CBN

Juyin Zamani: Yadda CBN ke ƙarfafa wa ɗalibai koyon ilmin sarrafa kuɗi, yayin da tattalin arziki ke sauyawa a zamanance 

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!