• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin samar da lantarki ta hasken rana na naira biliyan 3.8 a Jami’ar ADUSTECH da ke Kano

Wakilin Mu by Wakilin Mu
April 26, 2026
in Labarai
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta fara aikin samar da lantarki ta hasken rana na naira biliyan 3.8 a Jami’ar ADUSTECH da ke Kano
Babbar ƙofar Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote (ADUSTECH), Wudil, Jihar Kano

Babbar ƙofar Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote (ADUSTECH), Wudil, Jihar Kano

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Makamashi ta Ƙasa (ECN), ta ƙaddamar da aikin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana mai ƙarfin megawatt biyu (2MW) a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote (ADUSTECH) da ke Wudil a Jihar Kano.

Wannan aiki, wanda kuɗin sa ya kai naira biliyan 3.8, yana ƙarƙashin shirin nan na Renewed Hope Solarization na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Baya ga aikin samar da wutar, an kuma ƙaddamar da fitilun kan hanya guda 200 masu amfani da hasken rana a cikin harabar jami’ar.

Darakta Janar na hukumar, Dakta Mustapha Abdullahi, tare da Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha, Kingsley Tochukwu-Udeh, su ne suka ƙaddamar da aikin a ranar Juma’a.

Abdullahi ya bayyana cewa an ba kamfanin da zai gudanar da aikin wa’adin watanni uku kacal domin kammalawa.

Ya ce an tsara wannan aiki ne domin kawo ƙarshen matsalar tsadar wutar lantarki da jami’ar ke fuskanta, inda take biyan naira miliyan 22.4 a kowane wata.

“Wannan aiki na Wudil yana bin sahu ne bayan makamancin sa da muka ƙaddamar a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano a watan Satumba 2025, inda ake sanya tsarin megawatt huɗu (4MW), da kuma aikin da muka ƙaddamar a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) a makon jiya,” inji shi.

Kayan saka wutar lantarki ta hasken rana da aka kai jami’ar domin fara aikin

Ya ƙara da cewa an ba kamfanin Safiatu Global Resources Limited kwangilar a kan kuɗi naira biliyan 3.8, kuma ba za a ƙara ko sisi a kan kuɗin ba, sannan dole ne su kammala a cikin lokaci.

Binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa jami’ar tana da ɗalibai da ma’aikata sama da 24,000, kuma buƙatar wutar da take da ita ta kai tsakanin megawatt 12.3 zuwa 16.4. Sai dai, wutar da take samu daga kamfanonin rarraba wuta ba ta taka kara ta karya ba, yayin da janaretocin da take amfani da su ba sa iya ɗaukar nauyin buƙatar jami’ar.

A nasa jawabin, Minista Tochukwu-Udeh ya ce wannan aiki mataki ne na raya ƙasa a ƙarƙashin manufofin gwamnatin Tinubu na bunƙasa ilimi da ƙirƙire-ƙirƙire ta hanyar samar da ingantaccen makamashi.

Shi ma a nasa ɓangaren, Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Musa Tukur Yakasai, ya nuna jin daɗin sa da wannan gagarumin tallafi, inda ya ce wannan mataki zai ƙara bunƙasa harkar bincike da koyarwa a jami’ar.

Tags: ADUSTECHDakta Mustapha AbdullahiECNFarfesa Musa Tukur YakasaiKingsley Tochukwu-UdehlantarkimakamashisolarWudil
Previous Post

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

Next Post

Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

Gargaɗi, sharuɗɗa da wa'adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!